• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Idan Kana So Kaga Wauta, To Ka Bari Sai Wani Dan Arewa Marar Kishi Ya Zama Gwamna, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
February 5, 2023
in Ra'ayi
0
Idan Kana So Kaga Wauta, To Ka Bari Sai Wani Dan Arewa Marar Kishi Ya Zama Gwamna, Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya kai Dan uwa mai girma! Lallai idan kana so kaga wauta, tanbada da lalata, to ka bari sai Dan arewa marar kishin al’ummarsa ya zama Gwamna! Irin wannan mutum, zai dauki sarakunansa ba kowa ba, malaman addininsa ba kowa ba, ‘yan kasuwarsa ba kowa ba, talakawansa ba kowa ba, kai duk wani Dan arewa mai kishi a wurinsa banza ne, shirme ne, wanda bai kai kimar a girmama ra’ayinsa ba, ko a mutunta shi.

Jama’ah, abun mamaki, wani naga ya fito yana cin mutuncin ‘yan uwansa ‘yan arewa, kawai don ya samu kansa a gadon mulki, wanda wannan mulkin da yake kai, nan da wasu ‘yan kwanaki ya zama tarihi, ya zama abun tausayi, domin za’a wayi gari ba shine akan wannan kujere ba, wani ne.

Kuma shi wannan mutum, ya dauka cewa wai shekaru sune dattako, bai san cewa halin mutum da mutuncinsa da girmama na gaba da kyawawan halaye da dabi’u nagari, da tausayi, da jinkai, da kishi, da tausayin talakawa, da marasa karfi, da marasa galihu, sune ke sa a kira mutum dattijo, ba shekarun sa ba! Domin irin wadannan halaye ne magabatanmu, Allah ya jikansu, irin su Sardaunan Sokoto da su Tabawa Balewa da su Aminu Kano suka nuna, sai al’ummah ta kira su dattawa, ba shekarun su ba!

Kuma shi wannan gwamnan fa, mai cin mutuncin manya, wai da yake cewa sune dattawan arewa, har yana cewa shi shekarunsa sittin da uku, kasancewar ya dauka cewa shekaru sune dattako, kwanan nan fa aka nuna shi yana tika rawa, yana cashewa, yana rawar disko, yana lankwasa jiki, yana karairaya a fili cikin taron jama’ah, babu kunya babu tsoron Allah, amma wai a haka shi dattijo ne!

Wannan fa shine kadan daga cikin halayen wadannan mutane masu kiran kan su sune dattijai, wai!

Yanzu domin Allah, mu yiwa kan mu adalci, mu tambayi kan mu, shin ana dattijo a haka? Amsa wallahi ita ce, a’a.

Kai wani gwamnan ma kallon dattawan jiharsa yayi, bayin Allah, mutanen kirki, masu daraja da mutunci, masu nufin sa da kuma jihar su da alkhairi, iyayen wasu, kakannin wasu, wadanda kowa yasan irin gudummawar da suka bayar wurin ci gaban wannan kasa da kuma al’ummarsu, ya kira su da DATTAWAN WUKARI, yaci mutuncin su, ya fada masu maganganun banza. Menene laifin wadannan mutane? Kawai laifin su shine, sun ce a gyara, domin jihar su taci gaba, kowa ya amfana, amma don rashin kunya da rashin mutunci, ya kira su da dattawan wukari, kawai don ya samu dama, ya zama gwamnan jihar!

Ai su yarbawan da yake magana, ba zasu taba cin mutuncin dan uwansu Bola Tinubu irin haka ba, ko menene kuwa yayi masu, saboda me, saboda su duk matsayin da suka kai basa raina mutanensu da manyansu, kuma basa raina ra’ayin al’ummarsu, basa raina yankin su da mutanensu. Amma Dan arewa da ya zama Gwamna, to a lokacin shi yana ganin babu wanda ya isa, babu wanda ya isa ya gaya masa gaskiya, ko ya bashi shawara, ko ya tuntube shi ya nuna masa matsalolin yankinsa da halin da al’ummarsa suke ciki.

Duk wani mutum mai mutunci da yake kokarin jawo hankalinsa domin ya taimaki al’ummarsa, ko ya tallafa masu akan abun da zai amfane su, to ba zai saurare shi ba. Shi yasa, har kullun, zasu yi mulkin nasu na shekaru takwas, amma daga karshe su kare mulkin, amma arewar tana nan yadda take, babu wani ci gaba. Kai bama wannan ba, har ma zaka ce gara da kafin su hau mulkin, da halin da muke ciki a yanzu.

A Inda zaka fahimci hakan shine, don Allah, don Allah, don Allah, daga lokacin da aka dawo mulkin dimokradiyyah, wato 1999 zuwa yau, shin yankin arewa gaba yaci ko baya? Amsar ita ce, ko dan ubayyu yasan da cewa baya muka ci wallahi! Ba zaka fahimci haka ba sai ka san irin hasarorin da muka tabka sanadiyyar rashin tsaro, tun daga rikicin Boko Haram, rikicin kabilanci da na addini, rikicin fulani da makiyaya, rikicin barayin shanu da barayin mutane domin karbar kudin fansa; wanda wadannan rikice-rikice sun mayar damu baya sosai ba kadan ba, ta fuskar tattalin arziki da dukkanin sassa na rayuwar mu! Kuma wallahi duk wadannan rikice-rikice sun samu ne sanadiyyar rashin iya shugabanci da irin wannan dagawa, girman kai, da raina mutane na Dan arewa idan ya samu wani matsayi.

Yaku ‘yan uwana ‘yan arewa, ku sani, wallahi a halin yanzu, ba ku da makiya, masu kokarin ganin bayan ku, irin wasu daga cikin Gwamnoninku. Sune sanadiyya, kuma sune ummul haba’isun shiga cikin halin da kuke ciki na kunci da wahala a yau. Kuma gashi yanzu, sun taru, sun yi gungu, domin su yaki ra’ayin ku, su tursasa maku goyon bayan wadanda baku so su mulke ku.

Duk dai kun ga irin abunda suka yi wurin zaben fitar da gwani (wato primary election) na jam’iyyar su. Sun sayar da ra’ayin al’ummarsu saboda abun duniya.

To ku sani, a halin yanzu, abun nan da suka yi a wancan zaben fitar da gwani, shi suke so su maimaita irin sa, na sayar maku da ‘yancin ku da ra’ayin ku, da kuma mutuncinku, wato suna nufin dole ku amince da wanda suke son su kawo maku, kawai ba domin maslahar ku ba, a’a, sai dai domin cimma wasu maslahohi nasu na kashin kansu!

To wallahi, yaku ‘yan uwana ‘yan arewa, ya zama dole, tilas, kuma wajibi, mu fito fili karara, mu nuna masu bamu yarda ba! Yanzu ne lokacin da ya kamata mu fito mu yake su wallahi.

Daga karshe, mu dai fatan mu, da addu’ar mu, da rokon Allah mu shine, Allah ya bamu shugabanni na kwarai, nagari, wadanda zasu zama alkhairi ga Musulunci, gare mu, ga Nigeria, da ‘yan Nigeria, ga arewa, da ‘yan arewa da kuma al’ummah baki daya, amin.

Ku sani, ko tikitin Muslim-Muslim, ko tikitin Muslim-Christian, duk daya ne. Duk wanda mutum yayi ra’ayi zai zaba daga cikinsu yayi daidai, bai sabawa Allah ba, bai yi zunubi ba, bai yiwa kowa laifi ba. Domin dukkaninsu wallahi babu wanda zai yi hukunci da dokokin Allah da Manzonsa (SAW). Dukkanin su zasu yi hukunci ne da tsarin mulkin Najeriya (wato constitution).

Kuma kar mu saurari masu kokarin yin amfani da addini ko kabilanci domin su kawo muna tashin hankali da rikici. Irin su Babachir, da su Dogara, da kuma wasu Malaman addini, masu kokarin Musuluntar da Tikitin Muslim-Muslim, kuma su kafirtar da Tikitin Muslim-Christian, wadannan duk domin kan su suke yi, ra’ayinsu suke yi, ba domin maslahar al’ummar su ba ne!

Ina mai jan hankulan ku, tare da fada maku gaskiya tsakanina da Allah, cewa kar ku sake ku saurari wadannan mutane, wato Babachir da Dogara da kuma wadancan Malaman addinin, masu kokarin yaudararmu da cewa wai tikitin Muslim-Muslim addini ne, domin dukkanin su idan arewar ta rikice, aka fara kashe-kashe da kone-kone, wallahi ba zaka taba ganin ‘ya ‘yansu a cikin ko wace irin hayaniya ba. ‘Ya ‘yan talakawa ne kadai za’a yi ta kashewa a banza!

Sam bai kamata addini ya zama abun wasa ba. Bai kamata mu kawo maganar addini da kabilanci, muna kokarin haddasa gaba da kiyayya da rikice-rikice da tashe-tashen hankula da zubar da jinin bayin Allah a cikin al’ummah ba!

Haba don Allah! Addini ya zama bai da wata daraja a wurin ku sai an zo maganar siyasa, sai kuyi kokarin amfani da shi domin cimma wasu manufofinku?

Wallahi muji tsoron Allah. Kar mu yarda mu bayar da gudummawa wurin kara rugujewar arewa, da kara tarwatsa ta!

Magabatan mu irin su Sardaunan Sokoto, Tabawa Balewa, Ribadu, Isa Kaita, Aliyu Makaman Biddah, Dan Masanin Kano, Aminu Kano, Sa’adu Zungur, Abdur-Rahman Okene, da ire-irensu, ba haka suka yi ba wallahi.

Kuma mu sani, mu a arewa yanzu babu abunda ya rage muna sai mulkin nan, idan kuma muka yi sakaci, muka yarda ya sulale, to ya rage namu…!

Allah ya jikan magabatanmu, wasu daga cikin su suna cewa:

“MU HADU MUYI AIKI TARE, AMMA KOWA YASAN GIDAN UBANSA!”

Wannan magana tasu kuwa haka ta ke. Domin duk wani Dan arewa da yake zaune a wani yanki wanda ba nasa ba, yasan irin abinda yake gani a fili karara!

Kuma duk wani Dan Najeriya, da duk wani Dan arewa, yasan abun da yake ji a jikinsa, kuma mun san irin wuya da wahalar da muka sha karkashin wadannan mutanen. Don haka, ya zama tilas, dole, kuma wajibi, muyi amfani da damar da Allah ya bamu mu dakatar da su ta kowa ne hali!

Wahalhalun da muka sha sun isa haka nan. Dole ne mu canza wadannan mutanen da wasu, da kuma niyyah kyakkyawa, sai Allah ya taimake mu!

Idan kuma munki ji, to lallai ba zamu ki gani ba. Domin Malam bahaushe yace: JIKI MAGAYI!!!

Kuma Dan uwana ka sani, wannan ra’ayi nane, kuma fahimta tace, kai ma ban hana ka kayi naka ra’ayin ko taka fahimtar ba!

Allah yasa mu dace da shugabanni nagari, amin.

Dan uwanku: Imam Murtadha Muhammad Gusau – 08038289761. Juma’ah, 03/02/2023.

Tags: AbujaGwamnaHausaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

TINUBU A KAN SIKELIN 2023: Kada fa Asiwaju ya yi riginginen kunkuru a kan hanyar shiga Villa

Next Post

TA KACAME MASU: ‘Yaro na girme maka a aikin lauya’ – Raddin Keyamo ga Dogara

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
TA KACAME MASU: ‘Yaro na girme maka a aikin lauya’ – Raddin Keyamo ga Dogara

TA KACAME MASU: 'Yaro na girme maka a aikin lauya' - Raddin Keyamo ga Dogara

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZABEN SHUGABAN ƘASA: Kotu ta karɓi sakamakon zaɓen jihohi 17 daga hannun Peter Obi domin tantance sahihancin su
  • TSAKANIN ATIKU DA KEYAMO: Keyamo ya ɗaukaka ƙarar hukuncin tarar Naira Miliyan 10 da Kotun Tarayya ta danƙara masa
  • KOTUN ZAƁEN SHUGABAN ƘASA TA ƊAU ZAFI: Yadda Atiku ya kaɗa hantar Tinubu, APC da INEC a zaman shari’ar ranar Laraba
  • Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai
  • Sanatoci 67 sun rattaba hannu Yari suke so, da karin wasu na nan tafe – Inji Abdul Ningi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.