Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta ɗage zaɓen Sanatan Enugu Ta Gabas, biyo bayan bindige ɗan takarar sanatan shiyyar na LP da aka yi a ranar Laraba.
An dai yi wa Oyibo Chukwu kwanton ɓauna ne, aka bindige shi, kuma aka ƙone gawar sa.
Da ya ke bayyana yiwuwar ɗage zaɓen sanatan, Shugaban INEC Farfesa Mahmood Yakubu ya yi togaciya da Sashen Dokar Zaɓe na 34. Amma kuma ya ce INEC ba za ta yi hakan ba, har sai jam’iyyyar da abin ya shafa ta sanar da hukumar ga halin da ta ke ciki. Ya ce haka wani sashen dokar zaɓe ya ƙara yin bayani.
Yakubu ya ce idan aka yi hakan, to sai a yi zaɓen bayan kwanaki 14 da ɗagawar.
Wannan jarida dai ta buga labarin yadda aka bindige ɗan takarar sanatan jam’iyyar Peter Obi a Enugu
Wasu ‘yan bindigar da ba a san ko su wa ba ne sun bindige ɗan takarar sanatan jam’iyyar LP na Enugu ta Gabas, a yankin Amechi Awkunanaw, cikin Ƙaramar Hukumar Enugu ta Gabas.
An bindige Oyibo Chukwu ne a ranar Laraba, tare da wasu magoya bayan sa biyar waɗanda ke cikin mota ɗaya tare da shi.
Kisan ya faru ne kwanaki uku kafin zaɓen sanatoci, wanda za a yi tare da na shugaban ƙasa a ranar Asabar, 25 ga Fabrairu, 2023.
Shugaban jam’iyyar LP na Jihar Enugu, Casmir Agbo ya tabbatar wa PREMIUM TIMES a ranar Alhamis ɗin nan labarin wannan mummunan kisan gilla.
“E, gaskiya ce an bindige shi. A yanzu haka mu na zaman taron ganawa kan batun na mutuwar ta shi.”
Agbo ya yi zargin cewa kisan ɗan takarar na da alaƙa da siyasa, ba ‘yan bindigar da ba a sani ba ne.
Wata majiya mai kusanci da ɗan takarar da aka bindige ɗin, ya tabbatar wa wannan jaridar cewa tabbas an kashe ɗan takarar.
Ya ce bayan sun kashe shi kuma sun ƙone gasar sa.
“Babbar matsalar ita ce da ba shi da jami’an tsaro masu kare lafiyar sa. Haka ya ke kamfen ko’ina ba jami’an tsaro masu gadi ko kare lafiyar sa.”
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Enugu, Daniel Ndukwe ya tabbatar da labarin kisan, amma kuma ya ce a saurare shi sai an jima zai yi cikakken bayani.
Ba wannan ne karo na farko da aka kai wa ‘yan LP hari a lokacin kamfen ba.
A ranar 4 Ga Satumba, ‘yan bindiga sun kai wa mambobin LP hari a lokacin da su ke taro a Karamar Hukumar Awgu.
Haka ma a cikin Disamba sun kai irin wannan hari a jihar Imo.
Sai dai kuma wasu mambobin LP na zargin cewa wasu jam’iyyu ne ke ɗaukar nauyin hare-haren saboda haushin karɓuwa da farin jinin da LP ta yi.