• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

DA MAI LANƘWASA KO DA MAI GYAMBO?: Da wace ƙafar Atiku zai buga fenaritin gasar shiga Villa na ƙarshe?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
February 6, 2023
in Rahotanni
0
A gaggauta kama Atiku, a tsare shi a gidan yari sannan ya janye daga takarar shugaban kasa – APC

Sau uku tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya na buga gasar daga kai sai mai tsaron gida, wato bugun fenaritin gasar shiga Fadar Shugaban Ƙasa, amma bai taɓa jefa ƙwallo a raga ba.

Zaɓen da INEC za ta gudanar a ranar 25 Ga Fabrairu, zai kasance wata dama ɗaya tilo da ta rage wa Atiku ya jefa ƙwallo ɗaya tilo, domin ya samu nasarar zama shugaban ƙasa.

A matsayin sa na babban ɗan adawa ga jam’iyya mai mulki, za a iya cewa duk wata matsalar da APC ke ciki, to alheri ce ga Atiku. Gagarimar matsalar faɗan cikin gida da APC ke fama da shi, ƙasa da kwanaki 21 kafin zaɓen 2023, za ta iya zama tagomashi ga Atiku Abubakar.

To sai dai tun da farko PDP ta yi sakacin kasa ɗinke ɓarakar da Peter Obi na LP ya fusata har ya kauce daga PDP, ya tsaya takarar shugaban ƙasa a LP.

Irin hakan ne ya fusata Kwankwaso na jam’iyyar NNPP ya fice, ya samu takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin NNPP.

Duk da cewa mutanen Kwankwaso da na Obi a yanzu ba su cikin PDP, kuma jama’a sun ragu a jam’iyyar kenan. Sai dai kuma matsalolin da ake gaganiya kan su har ake jin haushin APC, ya sa PDP ta ƙara cika da hasalallun da ke jin haushin ƙuncin rayuwar da ake fama da ita kamar canjin kuɗi da tsadar fetur su na ta maida goyon bayan su kan Atiku, Kwankwaso ko Peter Obi.

Komawar ‘yar taratsi Najatu Mohammed ɓangaren Atiku bayan ta yi wa Tinubu wulaƙanci duk duniya ta shaida, hakan ya ƙara zaburar da Atiku, har ji ya ke yi kamar ya fara jin ƙamshin kujerar mulkin da Buhari zai sauka a kai ranar 29 Ga Mayu, 2023.

Sai dai kuma wani sabon ruɗani ya kunno kai daga kudancin ƙasar nan a farkon wannan wata na zaɓen 2023. Dattijo Shugaban Kungiyar Dattawan Neja Delta, Edwin Clark ne ya ce Gwamna Ifeanyi Okowa mai wa Atiku Abubakar takarar mataimakin shugaban ƙasa, ya fito ya janye takarar sa, kuma ya nemi afuwa.

Edwin ya ce Okowa ya ci amanar ‘yan kudancin ƙasar nan. Sannan kuma ya ce Atiku ba zai ci zaɓen 2023 ba.

Wata matsala da Atiku ke fama da ita, ita ce yadda ƙwararrun masu tsaron gida ke neman hana Atiku cin bugun ‘fanaritin sa’ na ƙarshe.

Wannan jarida a baya ta yi sharhin cewa a yanzu dai ko yaro na goye a ƙasar nan ya kwana da sanin cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP, Atiku Abubakar na cikin gagarimar matsalar da za a iya cewa ya janyo wa kan sa, tun bayan da ya yi gaban-gabarar watsi da shawarwarin manyan jam’iyya, ya ɗauki Gwamna Ifeanyi Okowa na Jihar Delta a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa.

Kusan gaba ɗayan manyan ƙusoshin jam’iyyar PDP sun cika da mamakin yadda Atiku ya yi watsi da shawarar da kwamitin fidda mataimakin shugaban ƙasa ya ba shi, cewa Gwamna Nyesom Wike ne na Jihar Ribas ya fi dacewa da kuma cancanta Atiku ya ɗauka takarar mataimaki.

Atiku ya hamɓare kwandon shawarar da aka ba shi, bayan da ya yi masu alwashin cewa zai yi aiki da shawarar ta su, ya ɗauki Okowa, ba tare da tuntuɓar su, ko sanar da su dalili ba.

Raddin Gwamna Ortom Kan Atiku: Ba Ni Da Tabbacin Zan Goyi Bayan Atiku A Zaɓen 2023:

Shugaban kwamitin mutum 17 da PDP ta kafa domin fitar wa Atiku Abubakar ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa, wato Samuel Ortom na Jihar Benuwai, ya fusata da yadda Atiku ya yi watsi da shawarar da su ka ba shi, inda ya ɗauki Ifeanyi Okowa a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa, maimakon Gwamna Nyesom Wike da su ka rattaba, su ka miƙa masa sunan sa.

Cikin wata tattaunawa da ARISE TV ta yi da Ortom a wannan makon, ya ce Atiku ya baɗa masu ƙasa a ido, ya yi watsi da matsayar da su ka ɗauka.

Wani ƙarin haushi a cewar Ortom shi ne yadda Atiku har yau bai tuntuɓi Wike ya ba shi haƙuri ba, kuma Atiku bai shaida wa kwamiti dalilin sa na ƙin ɗaukar Wike ba.

A kan haka ne Ortom ya ce shi fa a yanzu dai haƙiƙa ya dawo daga rakiyar Atiku, hankalin sa bai kwanta cewa zai goyi bayan zaɓen sa a 2023.

“Ba na jin zan goyi bayan takarar Atiku, amma dai zan ci gaba da yin addu’a idan Ubangiji na ya ƙaddare ni da mara wa Atiku baya, to shikenan sai na yi haka ɗin. Amma dai har yanzu kam ya fita daga harkokin gaba na.”

Ɗan Kudu Mu Ke So A Ba Takara, Ba Atiku Ba -Ayo Fayose:

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti Ayo Fayose ya fito ƙarara ya ce Atiku ya ci amanar Wike, don haka ba zai goyi bayan kamfen ɗin sa ba.

Wata gagarimar rigima ta kunno kai a cikin Jam’iyyar PDP, inda tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayo Fayose ya bayyana cewa Gwamna Nyesom Wike na Rivers da magoya bayan sa kakaf ba za su goya wa Atiku Abubakar baya a zaɓen shugaban ƙasa na 2023 ba.

A cikin wata tattaunawar musamman da Fayose ya yi da PREMIUM TIMES, Fayose ya ƙara jaddada cewa tabbas Atiku ya ci amanar Wike, don haka Wike da jama’ar sa za su zuba wa Atiku Ido, “tunda ya na ganin cewa shi kaɗai zai iya cin zaɓe, sai ya je ya ci ɗin.”

Fayose ya ce, “bayan Atiku ya yi nasara a zaɓen fidda-gwani, ya je har gida ya nemi haɗin kan Gwamna Wike, kuma ya yi masa alƙawarin zai naɗa shi ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa.

“Kuma da aka kafa kwamitin tuntuɓa wanda zai fito wa Atiku da ɗan takarar mataimaki, kwamitin ya bayar da sunan Wike.

“Amma da aka shiga aka fita, sai Atiku ya wancakalar da Wike, ya ɗauki Gwamna Ifeanyi Okowa na Jihar Delta.

“Atiku bai yi wa Wike mutunci ba. Domin bayan ya ci amanar sa ya ƙi ɗaukar sa mataimaki, ai ya-kamata ya kira Wike ya sanar da shi dalilin da ya sa ya karya alƙawarin da ya yi, wato ya ba shi haƙuri, amma Atiku bai yi hakan ba.”

Fayose ya ce har yau ya na na nan kan ra’ayin sa cewa kudu ya kamata ya yi mulki ya koma kudu a 2023.

“Yan Arewa na ganin Goodluck Jonathan bai kamata ya ci zangon ‘Yar’Adua daga 2015 zuwa 2019 ba. Saboda haka sai su ka kori Jonathan ta hanyar zaɓen Buhari a ƙarƙashin APC.

“To tunda Buhari ya kammala shekarun sa takwas, ya kamata a yi adalci a bai wa ɗan kudu mulki, ba wai a ce Atiku ne daga Arewa zai fito neman zama shugaban ƙasa ba.

“Ni ina da tabbacin cewa ko kamfen Wike ba zai taya Atiku ba. Mu da ke goyon bayan Wike, duk wanda ya ce mu zaɓa shi za mu zaɓa, amma ba zai taɓa cewa mu zaɓi Atiku ba.”

PREMIUM TIMES ta tuntuɓi Kakakin Yaɗa Labaran Atiku, mai suna Paul Ibe. Ya ce ya kamata a daina gunguni da ƙulafuci, a haɗa kai a yi nasara, a kori APC.

Zafin Duka Da Gudumar Da Obasanjo Ya Yi Wa Atiku Bai Daina Yi Masa Raɗaɗi Ba:

CIkin makon jiya ne tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa a rayuwar sa ya tafka manyan kura-kurai biyu.

Ɗaya daga cikin manyan kura-kurai biyu da ya ce ya yi a rayuwar sa, shi ne ɗaukar da ya yi wa Atiku Abubakar a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a lokacin takarar zaɓen 1999.

Wannan kalami tabbas bai yi wa Atiku daɗi ba, wanda a yanzu haka ya lula Dubai ya bulaguro a can.

Kaushin da haushin wannan kalamin ne ya sa Shugaban Dattawan PDP Walid Jubrin ya bai wa Obasanjo sa’o’i 48 cewa ko dai ya janye kalaman da ya yi kan Atiku, ko kuma Jubril ɗin shi ma ya fallasa Obasanjo, duniya ta ji wani mummunan aibi kan sa.

Har ila yau Atiku na shan suka kan zarge-zargen baya da aka sha yi masa musamman wajen wai da hannun sa a afkuwar wasu manyan matsalolin ƙasar nan, musamman sayar da wasu kamfanonin gwamnatin tarayya a lokacin da ya na mataimakin shugaban ƙasa.

Sannan kuma duk da rashin farin jinin da APC ke fama da shi a yanzu bayan ta shafe shekaru bakwai kan mulki, tare da kasa magance matsalolin ƙasar nan, ba a daina yi wa PDP kallon musabbabin haddasa matsalolin a shekaru 16 ɗin da ta yi ta na mulki tsakanin 1999 zuwa 2015 ba.

Tags: AbujaAtikuHausaLabaraiNewsPDP
Previous Post

A’isha Buhari na cikin gungun masu-hana-ruwa-gudu a Fadar Shugaban Ƙasa – Naja’atu Mohammed

Next Post

Emefiele ya ƙirƙiro canjin launin kuɗi don ya haddasa fitinar da za ta hana yin zaɓen 2023 – Oshiomhole

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Adams-Oshiomhole

Emefiele ya ƙirƙiro canjin launin kuɗi don ya haddasa fitinar da za ta hana yin zaɓen 2023 - Oshiomhole

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ganduje ya bar wa Kano bashin Naira biliyan 241, Abba ya ce zai bi ya gano hanyoyin da aka ciwo bashin
  • Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare
  • JAWABIN BANKWANA: Ba a taɓa gwagwagwar zaɓen shugaban ƙasa kamar na 2023 ba – Buhari
  • JIGAWA A HANNUN BADARU: Yadda shekaru takwas na mulkin APC ya kasa rage katutun talauci da fatara
  • BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.