• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Alheri Ɗanƙo Ne: Daɗaɗɗen Zumuncin Da Ke Tsakanin Tinubu Da Arewa, Daga Abdulaziz Abdul’aziz

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
February 22, 2023
in Ra'ayi
0
Alheri Ɗanƙo Ne: Daɗaɗɗen Zumuncin Da Ke Tsakanin Tinubu Da Arewa, Daga Abdulaziz Abdul’aziz

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ya yi wani taƙaitaccen jawabi, amma fa mai ratsa jiki sosai, a lokacin da ya ke gabatar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Zulum cewa ya yi Tinubu bai yi watsi da Jihar Barno ba a lokacin da jihar ke cikin matsanacin halin da ba ta samu kan ta a tsawon shekaru 1,200 na tarihin Barno ba. Yayin da wasu da dama su ka juya baya daga ziyarar Maiduguri, saboda ganin ta zama wani filin gumurzun Boko Haram, shi kuwa Asiwaju Tinubu ya nuna juriyar kai ziyara can, ba sau ɗaya ba, ba kuma sau biyu ba.

Zulum ya ci gaba da yi wa Shehun Borno bayani, “Lokacin da Borno ta shiga mawuyacin hali, Tinubu ya sha kawo ziyara, kamar sau bakwai ko sau takwas a cikin shekaru sha ɗaya. Kuma ina tabbatar maka babu wani da ya yi mana haka, sai dai shi.”

Wannan kyakkyawar shaida da Zulum ya bayar kan Tinubu, ba a shekarun baya-bayan irin wannan zumuncin ya ƙullu tsakanin sa da Arewacin Nijeriya ba. Ba zumunci ba ne na ‘yan a-rama-wa-kura-aniyar-ta ba. Zumunci ne na abokantaka da kyakkyawar zamantakewa. Shi ya sa ba wani abin mamaki ba ne ganin irin gagarimar karɓuwar da Asiwaju ya yi a Arewa.

Babbar alamar gane irin karɓuwar da ya yi a Arewa, ita ce irin cincirindon jama’ar da ke fitar-farin-ɗango zuwa wurin kamfen ɗin sa a jihohin Arewa. Tun daga Kaduna, tsohuwar hedikwatar Arewa zuwa Kano, cibiyar kasuwancin Arewa, har zuwa daulolin mashahuran sarautun gargajiya biyu na Arewa, wato Daular Fulani ta Sokoto da kuma Borno, Daular Kanuri.

Mamaki ya kama wani yayin da ya ga hoton dandazon mutanen da su ka halarci ɗaya daga cikin wuraren kamfen ɗin Asiwaju a Arewa. Sai ya shiga shafin sa na tiwita cike da al’ajabi, ya rubuta cewa: “Yan Arewa fa sun fi kowa ɗaukar batun Tinubu da muhimmanci.” To ai kuwa maganar sa gaskiya ce, saboda ‘yan Arewa sun iya bayar da gaskiya da amanna ga abu mafi cancanta. Na biyu kuma shi ne sun yarda wannan ne lokacin da ya fi dacewa su nuna wa Tinubu godiyar su dangane da daɗaɗɗe kuma kyakkyawan zumuncin da ke tsakanin su.

Dalili kenan duk wani haƙilo da kitimirmirar da ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP, Atiku Abubakar da ‘yan-koren sa su ka yi ta kitsawa domin ruruta ƙiyayyar ƙabilanci da ɓangaranci, ba su yi nasara a Arewa ba. Saboda mafi yawan mutane ba su ɓata lokacin sauraren su, ko maida hankali a kan su ba.

Tambayar da kawai mutane ke yi a batun masu neman shugabancin ƙasa, ita ce shin ne ɗan takara wane ya taɓa yi wa Arewa da jama’ar ta, har zai cancanci su zaɓe shi? Hakan kuwa ai mutane sun yi gaskiya, domin za su fi so a ce su na tare da wanda a duk lokacin da su ke cikin wani hali, shi ya na tare da su, ba ya gudun su kamar yadda wasu ke yi a Arewa, sai ranar neman biyan buƙatar mutum sannan zai wanke riga ya garzaya Arewa.

Tarihi ko na ce labarin daɗaɗɗiyar alaƙar kusancin Asiwaju da Arewa ya na da tsawo sosai. Sai dai na ɗan yi tariyar baya kaɗan na ɗan taƙaita. Saboda hatta ita kan ta farkon tafiyar Tinubu bisa turbar siyasa, daga Arewa ya fara ta ɗungurugum. A lokacin da aka fara siyasar rusasshiyar Jamhuriya ta Uku, sai Tinubu ya shiga rundunar siyasar marigayi Shehu ‘Yar’Adua, a lokacin da ɗan ƙabilar sa Lateef Jakande shi ma ya fito takara.

A shekarar da marigayi MKO Abiola ya fito takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashin SDP, Tinubu ya taka muhimmiyar rawa wajen ɗaukar Babagana Kingibe a matsayin mataimakin takarar Abiola.

A baya-bayan nan kuma, Tinubu ya ɗauki gaban-gabarar nuna cikakken goyon gaba ga ‘yan Arewa masu takarar shugabancin ƙasa, har sau huɗu ɗaya bayan-ɗaya, a lokuta daban-daban.

Asiwaju ya goyi bayan Atiku a 2007, sai Nuhu Ribadu a 2011, ga Muhammadu Buhari har sau biyu, a 2015 da 2019. Waɗannan kenan, banda ma wasu masu ɗimbin yawa da ya tallafa wa su ka samu matsayi ko nasarar muƙamai, ba don wata biyan buƙata ba. Amma da ya ke ɗan Adam saurin manta baya gare shi, Atiku da Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto ai duk sun ci albarkacin Tinubu a 2011. Domin Asiwaju ne ya shiga gaban bataliyar da ta ciwo wa Tambuwal yaƙin da ya kai shi yin nasarar zama Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa a 2011.

Idan mu ka fita daga batun siyasa kuwa, Tinubu a koda yaushe ya na tare da Arewa a duk lokacin da yankin ya shiga mawuyacin hali. Ya na ɗaukar matsalar da muhimmanci, tamkar shi ma ɗan Arewa ne cikakke. Kuma hakan ya ke nunawa a sauran yankunan ƙasar nan baki ɗaya, ta hanyar ɗaukar nauyin magance abin da bai fi ƙarfin iyawar sa ba. Ya je har Zamfara da Birnin Gwari ya jajenta wa waɗanda ‘yan bindiga su ka ƙuntata wa, ya ƙarfafa masu guiwa, kuma ya bayar da tallafi. Banda Asiwaju babu wanda ya je irin waɗannan wuraren sai fa da ƙafar su ta kai su lokacin kamfen.

A kwanan nan da zaɓen shugaban ƙasa ya kusanto, ‘yan adawa na ta gaganiya da kiciniyar shafa wa Tinubu baƙin fenti. Sun ƙirƙiri ƙarairayi sun yaɓa a kan sa. Mutumin da ya kashe kaifin hargagin ‘yan OPC a Legas, kuma ya mutunta Hausawa mazauna Legas, wai shi ‘yan adawa ke zargi da kishiyar abin da ya yi.

Ku tuna lokacin da Tinubu ya je Dakin Taro na Arewa House, Kaduna, ya yi maganganun da su ka ratsa jini da jijiyoyin dattawan Arewa, ciki kuwa har da ‘yan ga-ni-kashe-nin Atiku, to duk wasu ‘yan jagaliyar da a yanzu za su fito su ce wai Tinubu ba shi da wani daftarin bunƙasa Arewa ai sun makara.

‘Yan Arewa mazauna Legas sun fito sun bayyana yadda Tinubu da tsare-tsaren da ya aiwatar ya kai su ga samun damar da su ka samu karsashin rayuwa sosai a Legas. A yanzu haka akwai Bakatsine kwamishina a Jihar Legas, wanda wannan al’adar kuwa Tinubu ne ya fara ta, ya assasa ta. Kuma an zaɓi wasu da dama an ba su matsayi daban-daban. Miliyoyin ƙananan yara ‘yan Arewa sun amfana da tsarin bayar da ilmi kyauta da Tinubu ya ƙirƙira a Legas.

Da farko ‘yan adawa sun fara da yarfen cewa Tinubu ba shi da cikakkar lafiya. Amma sai ya kunyata su ta hanyar zirga-zirgar fita kamfen ɗin da ya ke yi da har yau bai sare ba, bai nuna gajiyawa ko kasala ba.

Saboda haka tunda yanzu ƙaryar ‘yan adawa ta ƙare, lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su zaɓi ɗan takarar da za su iya damƙa wa amanar kan su da ƙasar su, wanda ya ke da tarihin aiwatar da gagarimin ayyukan ci gaba, wanda ya taɓa shafe tsawon lokaci ana cin moriyar ayyukan ci gaban da ya samar a zahiri.

Asiwaju na da kyawawan alamomin samun nasara a zaɓen da za a gwabza ranar Asabar. Saboda ya na da ɗimbin magoya baya, waɗanda ba su bayar da kai borin masu yaɗa siyasar ƙabilanci ya hau kan su ba.

Arewa dai ba ta manta da irin zumunci, abota da kyakkyawar alaƙar ta da Tinubu ba. Mutanen yankin sun tabbatar da cewa su ba al’ummar da ke rama alheri da sharri ba ne. Dalili kenan ma su ka shirya tsaf, zaman jiran zuwan ranar zaɓen shugaban ƙasa, domin su rama wa Tinubu alheri da alheri.

Abdulaziz shi ne Mataimaki Na Musamman A Fannin Yaɗa Labarai, na Asiwaju Tinubu.

Tags: AbujaAPCArewaAtiku AbubakarFulaniLabaraiNewsNuhu RibaduPDPSokotoTinubu
Previous Post

2023: PDPin Ribas ta ce Amaechi na cikin makusantan Buhari da su ka jefa ‘yan Najeriya cikin rayuwar ƙunci

Next Post

ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Ƙungiyar Ƙwadago, NLC ta umarci ma’aikata su zaɓi Peter Obi

Next Post
Ni fa mutane irin su El-Rufai addu’a kawai nake yi musu Allah ya shirya su – Martanin Obi ga El-Rufai

ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Ƙungiyar Ƙwadago, NLC ta umarci ma'aikata su zaɓi Peter Obi

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 11 da ake so a yawaita yi a watan Ramadan
  • ZABEN KADUNA: PDP ta yi murdiya a wasu kananan hukumomi, zan Kalubalance su a Kotu – Uba Sani
  • SABUWAR ƁARAKA A PDP: An dakatar da Fayose, Anyim, Gwamna Ortom zai gurfana gaban kwamitin ladabtarwa
  • Yunƙurin ‘yan majalisar APC uku masu so a halasta tu’ammali da tabar wiwi ya samu cikas
  • ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Keyamo ya roƙi SSS su kama Obi da Datti, saboda furucin cewa ‘zaɓen 2023 daidai ya ke da mulkin soja’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.