Mazauna kauyukan ‘yan bangan da aka kashe sun bayyana cewa adadin yawan mutanen da suka mutu a harin da ‘yan bindiga suka kai ya zarce mutum 102 a ranar Lahadi.
Dagacen kauyen Guga da baya so a fadi sunnan sa saboda tsaro ya faɗi a ranar Litinin cewa sun yi jana’izar mutum 72 da suka mutu a dalilin wannan hari na ranar Lahadi da yamma.
Wani mazaunin kauyen Kakumi, Najibu Aminu ya faɗi wa PREMIUM TIMES cewa wannan hari ya yi matukar tsorata mutane a kauyukan su.
“Babbar matsalar da muke fama da shi shine na rashin makamai domin gwamnati a kwanakin baya ta karɓe mana makamai a lokacin da ake yarjejeniya yin sulhu tsakanin mu da ƴan bindiga.
“Muna fargaban cewa ‘yan bindigan za su dawo su kara kawo mana hari.
Kauyukan da suka fi fama da hare-haren ‘yan bindiga sun hada da Garangozai, Gidan Wawu, Gidan Sarkin Noma, Gidan Tanko, Layin ‘Yannehu, Unguwar Ɗanbaushi, Gidan Kanawa, Unguwar Gero, Unguwar Ɗaga, Maiyaɗiya, Gangare, Gidan Cirai, Gidan Bawa, Gidan Aminu, Gidan Baushi da Gidan Gagare.
Allah -wadai da harin ƴan bindiga – Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari ya yi Allah–wadai da ‘yan bindigar da su ka kashe ‘yan sakai 42 a Jihar Katsina.
Ita ma Gwamnatin Jihar Katsina ta ce za ta kafa kwamitin da zai binciki musabbabin kisan ‘yan sakai ɗin.
Cikin wata sanarwa da Garba Shehu, Kakakin Yaɗa Labaran Shugaba Buhari ya fitar a ranar Lahadi, ya ce Buhari ya yi matuƙar jimamin kisan mutanen 42, kuma ya miƙa ta’aziyya ga iyalan su.
Buhari ya ce waɗanda ‘yan bindigar su ka kashe, mun yi mutuwar shahada, tunda an kashe su a ƙoƙarin kare maɓarnata afkawa ƙauyen su.
“Mu na jimami da addu’a da kuma ta’aziyya ga iyalan ‘yan sakai waɗanda ‘yan bindiga su ka kashe. Allah ya gafarta masu.” Inji Buhari.
Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana sanarwar kafa kwamitin gano musabbabin kisan ‘yan sakai ɗin su 42.
Mashawarcin Harkokin Tsaro na Gwamnan Katsina, Ibrahim Katsina ne ya bayyana haka ga manema labarai a ranar Asabar da dare, yayin da ya ke magana kan wannan kisan gillar.
Ibrahim, wanda tsohon jami’in SSS ne, ya ce an kashe ‘yan bindiga da dama a mummunan gumurzu.
Ya ce maƙasudin kafa kwamitin shi ne domin ya gano abin da ya kai ga yin wannan mummunan kisan gilla.
Yadda Aka Yi Kisan Gillar ‘Yan Sakai 42 A Katsina:
Rundunar ‘Yan Sandan ta fitar da sanarwar yadda aka yi kisan gillar.
Kakakin Yaɗa Labaran ‘Yan Sandan Katsina, Gambo Isa, ya ce ‘yan an kai hari ne ranar Laraba da dare a ƙauyen Kandarawa, inda su ka dira gidan wani tattajirin kauye, kuma ɗan kasuwa, cikin Ƙaramar Hukumar Bakori, su ka kwashi shanu 80.
“Sun kai hari ne gidan Alhaji Muntari a Unguwar Audu Gare, cikin garin Kandarawa. Sun buɗe wuta tare da kama shanu 50 tumaki 30.”
Gambo Isa ya ce wannan hari da aka kai ya harzuƙa ‘yan sakai, waɗanda su ka yi shiri su ka bi ‘yan bindigar su ka fara musayar wuta, a ƙoƙarin su na ƙwato dukiyar da aka sata.
“A ranar 2 Ga Fabrairu kuma sai wajen ƙarfe 10 na dare ‘yan sakai daga ƙauyuka 11 su ka yi gangami su ka nausa farautar ‘yan bindigar.
“Sun bi sawun ‘yan bindigar har Dajin ‘Yargoje. Sai dai abin takaici ba su sani ba ashe ‘yan bindigar sun yi masu kwanton-ɓauna, su ka bindige mutum 41, biyu kuma su ka ji raunuka.”
Discussion about this post