A 27 ga watan Mayu ne na shekara 2022 ranar Juma’ah a ka bayyana cewar Malam Umar Namadi ne, Mataimakin Gwamnan Jigawa aka bayyana ya lashe zaben fidda gwani na Jama’ iyar APC da kuri’a 1,220 daga cikin kuri’u 1,420 da aka kada, Mutane 9 ne suka nemi kujerar Gwamnan Jigawa a karkashin jama’iyar APCn.
Faruk Adamu Aliyu kwararren dan siyasa ne da ya shahara a Nijeriya, ya tabaa zama shugaban marasa rinjaye a majalissar dokoki ta kasa. Faruq Adamu yana daga cikin wanda a ka taba kadawa kuri’a ta kiranye da ga majalissa, a lokacin da suke takon saka da tsohon gwamnan Jigawa Alhaji Saminu Turaki, amma ba’ayi nasarar dawo da shi daga majalissar ba.
Duk da cewa Faruq Adamu Aliyu, tsohon Shugaban Marasa Rinjaye a Majalissar wakilai yazo na uku (3) ne a zaben, amma bai gamsu da sakamakon ba, har ta kai ya tafi Kotu don kalubantar wannan zabe. Faruq Adamu Aliyu duk da rashin nasarar karar da yayi a babbar Kotu, wato High Court dake Jigawa, ya sake daukaka kara zuwa kotun gaba, wanda a ita ma Kotun bai samu nasara ba, bai hakura ba, ya sake daukaka kara zuwa Kotun Koli wato Supreme Court, wanda ita ma Kotun Kolin a 13 ga wannan watan nan ta yi watsi da karar da Faruk Adamun ya shigar.
Wannan hukuncin ya tabbatar da nasarar Malam Umar Namadi, wannan hukuncin yamkuma kawo karshen wannan danbarwa, kuma ya kawo wa ita kanta jama’iyar APCn kwanciyar hankali da kuma tsayawa wuri guda da maida hankali akan zaben duk gari.
Faruq Adamu Aliyu, wanda a ke gani shine Jagorar wato Party Leader na Jama’iyar APC a Jigawa, ba kawai a Jigawa yana daga cikin jigogin da suka kafa ita kanta Jama’iyar, kuma a na ganin sune na kusa-kusa da Shugaba Buhari a cikin mutanen APC, Faruq wanda suke tare da Shugaba Buhari tun daga ANPP, CPC har kawo wannan lokacin da aka yi maja a ka samu APC.
Sai dai a wannan karnin na APC, Faruq yayi takara kusan sau uku kenen a cikin jama’iyar APC ba tare da samun nasara ba. Faruq yayi takarar Mataimakin Shugaban Jama’iyar APC na kasa har karo biyu amma bai samu nasara, hatta a wannan karon na karshe, a na rade-radin cewa yana daga cikin mutane biyar da Shugaba Buhari ya nema a basu mukami a cikin Jama’iyar , amma hakan ma ta gagara.
Shin a kwai darussa a cikin wannan Shari’a?
Babban abin alfahari ga Dimokaradiyya shine yadda Doka da Oda suka samu yin walwala, kowa ya samu dama ikon bibiyar hakkin sa, a duk lokacin da yake zargin an danne masa. Matakin da Faruk Adamu ya dauka, ya nuna cewar, kowane dan Jama’iyya na da ‘yancin bibiyar hakkin sa a dokance.
Tabbas a kwai darussa a wannan mataki da Faruk Adamu Aliyu ya dauka, kasancewar, wannan ne lokaci na farko da a ka ga irin wannan lamari daga cikin manyan Jama’iyyu a Jahar Jigawa, wanda wannan ya nuna yadda a ka soma samun cigaban siyasa, da samun yancin dan jama’iyya ya kalubalancin sakamakon ta hanyar doka da oda.
Wani darasin a cikin wannan shari’a shine, yadda ba a samu wani rabuwar kai a tsakanin manya da kananan yan jama’iyar ba, tun da ga farko har karshe, kusan za a iya cewa APC a Jigawa tafi ko ina zaman lafiya. Abin sha’awa shine yadda dukkanin wannan shugabanni suka nuna kwarewa a siyasance, ta wajen ta wajen fahimta da kuma tarbiyantar da magoya bayan su, aka zauna lafiya, har a ka kawo karshen wannan shari’a.
Ko ba komai wannan zai sanya shugabanni ko jagororin siyasa, suna kiyaye wajen yin abin da ya dace bisa doka da ka’ida, sannan ya hana kama karya, domin cewa a yau kowa zai iya daukar matakin shari’a, duk lokacin da ya kasa gamsuwa ko zargin kin yin adalci a wajen zabubbka na cikin gida ko makamantan su.
Rungumar hukuncin da Faruq Adamu Aliyu yayi, da kuma cewar zai taimakawa jama’iyar da abokin takarar sa Malam Umar Namadi wajen ganin yayi nasara a zaben sa, dama duk yan takarar su na APC, wannan ma, wata kwarewa ce a siyasa na karbar kaddara da nuna juriya da kuma yadda da bin doka.
Dama abin da yafi dadi a Dimokaradiyya shine kowa ya samu yancin yin walwala, sannan kuma ya samu damar bibiyar hakkin sa a dokance.
Wannan darasi ne wanda yan uwa matasa yan siyasa ya kamata su dauka.
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post