Kotun Grade 1 dake Karu a Abuja ta yanke wa Oto Obong mai shekaru 33 hukuncin zaman kurkuku bayan ta kama shi da laifin yi wa wata mata dukan tsiya.
‘Yan sanda sun kai karar Obong dake zama a kwatas din Mpape kotu bisa laifin ji wa wata mata rauni a jiki a sandiyyar dukan da ya lakada mata.
Alkalin kotun Umar Mayana ya hana bada belin Obong sannan ya ce za a ci gaba da shari’a ranar 6 ga Fabrairu.
Mayana ya ce a dalilin haka ya yanke hukuncin daure Obong a kurkukun dake Keffi.
Lauyan da ya shigar da kara Ade Adeyanju ya ce an kai karar laifin da Obong ya aikata ne a ofishin ‘yan sandan dake Maitama a Abuja.
Bisa ga karar da aka shigar ya nuna cewa an ga lokacin da Obong ke lakada wa wata mata mai suna Elizabeth Aguru dake zama a Wuse II a titin Ademola Adetokunmbo Crescent dukan tsiya kuma ta ji rauni a hannu da kirjinta.
Garin dukan da Obong ya lakadawa Elizabeth ta zubar da kudinta har naira 7,000 sannan da hular gashi da ta saka na naira 35,000.
A kotun Obong ya musanta laifin da ake zarginsa da shi.
Sai dai kotu bata saurare shi ba ta tsare shi sannan ta ce za a cigaba da karar bayan an kammala bincike akai.
Discussion about this post