• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RIGIMAR AISHA BUHARI DA DALIBI AMINU: Ko Talakan Arewa Zai yi Karatu a Kan Soyayyar Sa ga Buhari, Daga AA Ilallah

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
December 3, 2022
in Ra'ayi
0
RIGIMAR AISHA BUHARI DA DALIBI AMINU: Ko Talakan Arewa Zai yi Karatu a Kan Soyayyar Sa ga Buhari, Daga AA Ilallah

Duk da cewar First Lady Aisha Buhari ta fuskanci kalubalen da ke cikin matsayin da ta dauka a baya, na neman hakkin ta, bisa zargin cin mutuncin da Dalibi Aminu (aka Catalyst) na Jami’ar FUD yayi mata a Dandalin Twitter, wanda a yanzu ta ce ta janye kuma ta yafe masa, amma fa duk da haka wannan hatsaniya ta bar baya da kura. Ko yanzu talakawan Arewa zasu sake fahimtar matsayin su a wajen Baba Buhari? Wanda a baya suke ganin sa tamkar wani waliyi mai ceton su.

Duk da cewa a yanzu ta fahimci gaskiyar yin afuwa da juriya har ta janye kudirin ta, ko kadan wannan hukuncin da First Lady ta dauka a baya, kan shaguben da wannan Dalibi yayi mata, babu wani abin mamaki.

Kuma a matsayinta ta mutum da ke son kare mutuncin ta, tana da uzuri tabi kadun hakkin ta a gaban kuliya, saboda haka babu wani abin mamaki a ciki. Amma in har ta tabbata a turbarta ta neman hakin ta lakada masa duka, in har haka abin yake, to ba tayi dattako ba, a matsayin na uwa. Bayan haka babban abin takaicin shine yin gum din Shugaba Buhari a kan lamarin a baya, har sai da wannan batu ke neman tono garma, sai nan a ka ce ya magantu. Wanna fa, ya isa ya nunawa Talakan Arewacin Nijeriya matsayin sa a gida Baba Buharin da bashi da gata a baya kamar na talakan.

Wai shin da talakan Arewacin Nijeriya suna tunanin Shugaba Buhari na kaunar su kamar yadda suke yi masa? Talakawa ne gatan sa, su suka tsaya masa, har wasu suka rasa rayukan su, su suka bashi kudin da ya kaishi Villa, har ma Aisha ta zama First Lady. Inda da irin wannan kauna da bai bar wannan matsala ta kai haka ba. Kai, in da a ce talakan arewa na da matsayi a gidan Buhari da haka bata faru ba.

In har muka yi tunani a baya da ma a yau, da Buhari na kaunar talakan Arewa da bai yi sake a mulkin sa Takin Zamani ya ya kai N20,000 da ga N3,000, amma kullum gori yake musu suna sharholiya basu noma.

Inda akwai kauna, bazai yadda arewa maso gabas ta daidaice ba, matasan su sun dunguma jeji, sun zama yan ta’adda, sun hana noman ma a yi.

Inda da wannan kauna bazai hana dan talaka karatu ba, irin na jami’a, amma wannan batu na gaba kowa zai sheda, domin kamar yadda yayi ikirari, dan talaka irin na arewa bai isa karatu a jami’a ba, misali a tambaya nawa ne dalibi zai biya a sabuwar jami’ar tarayya da ya kirkiro a garin Azaren Jahar Bauchi. To wannan shine shirin Buhari ga dukkanin makarantun gaba da sakandare, wannan duk sakayya ce ga talakan Arewa daga Buhari. A nan gaba sai duk dalibin da ke son karatu a Jami’a ya biya kimanin N200,000 koma fiye a kowace shekara, wannan kiyasine sakamakon rigimar gwamnati da ASUU, kuma shine matsayar Gwamnatin Buhari.

In muka muka tuna baya, siyasar kauna da mutanen Nijeriya, musamman ma na Arewa, kuma matasa suka nunawa Buhari a baya, babu irin cin zarafi, da shagube a kafafen sadarwar zamani da mawakan zamani basu yiwa shugabannin wancan zamanin ba, don kawai a tallata Buhari. Amma su sun nunawa ‘Yan Nijeriya Juriya, kawaici da sanin ya kamata, babu wani shugaba ko matar sa da nuna irin wannan fushin. Amma yau gashi halin da muke ciki da gidan Shugaba Buhari, wanda karara suka nuna rashin juriya da hakuri a kan kalaman da basu kai sun kawo ba, kuma Magana mai harshen damo, wanda bai zama lalle abin da Aminu yake nufi yayi dai dai da fassarar ka/ke/ko ni ba.

In mun dawo kan takaddamar nan. A Siyasan ce, ita fa siyasa duk wanda ya shige ta, to ya zama dole yayi hakuri da abubuwa masu yawa, wannan ya hada kananan maganganu da ma manyan maganganu, dole sai kaji, kayi kamar baka ji ba, wani lokacin in angayama mai daci, sai ka cije, kama yi dariyar getsetse.
Irin wannan maganganu an gaya wa shugabannin baya, amma yi musu zancen da wuce haka da su da iyalen su, kai har ma a irin kasashen da suka ci gaba a siyasa irin su USA a na yi wa shugabannin irin wannan maganganu. Aisha Buhari yar siyasa ce, domin da ita aka yi neman zaben mijinta, har ta jogoranci wasu tarurrukan a baya, ya kamata irin wannan maganganu su zama darasi ga gidan kowace siyasa.

A yau fa Aisha Buhari, ita ce First Lady, har an nada mata masu hidima da taimakamata wajen aikace aikacen ta, kuma duk ana biyan su da kudin talakawan Nijeriya. Koda a fagen siyasa, wadda ita wannan siyasa ta maida Aisha Buhari First Lady, harma take jagorantar wasu matan shugabannin kasashen Africa, siyasa ce ta bata damar shiga Villa, har ma tasa a jawo aka yi mata tsabiri irin na siyasa a Dandalin Twitter. A tarihin siyasar wannan kasa fa, babu shugaban kasar da ya more mulki, wajen aurar da yayan sa, da kasetacchen buki na kece reni kamar Buhari da matar a Aisha Buhari. Dole yayin da ake shan zaki, wani lokacin a dandani dachi, haka mulki ya gada.

A Addinance ma, kowa ya san muhimmancin yin hakuri, yafiya, afuwa da maida alkhairi ga sharri, kullum irin wannan kalamai malamai ke yiwa al’ummah, musamman talakawa, amma abin mamaki, a magangannun malamai a yau, saboda abin ya shafi masu mulki, amfi karfafa rashin tarbiyar wannan yaron akan aja hankalin shugaba ya zama abin musali wajen yin afuwa da yafiya, kamar yadda Malamai suka nuna annabi yafi kowa hakuri da afuwa, wannan afuwa da tayi, tamkar tayi koyi da Manzon Tsira ne.

Ita kanta First lady inda ta nuna dantako da kuma zama uwa ta gari kamar irin su Nana Aisha (RA) matar Manzon Allah (SAW) da ta jawa Aminu Kunne da yi masa nasiha da kuma ilmantar da shi a kan kwawawan kalamai, da har abada ta zama abar musali a cikin al’umar wannan lokaci, da ma wanna surutan basu faru ba. Aminu (Catalyst) ba yaron banza bane, yaron da yake Ajin karshe a Jami’a, ya kamata a yi masa uzuri, domin babu wanda ya fi karfin kuskure. Amma duk da haka ba a makara ba, duk da cewa daga baya tayi afuwar.

In na dawo kan batu na, cewa dama talakan Arewa ne ke yaudarar kan sa a kan san Buhari, shi daman ba talaka a gaban sa, kuma kauda kai ya keyi, harma yayi dariya a wasu lokutan in talaka ya shiga matsi, wannan batu na Aminu kawai daya ne, ganin cewa an makara, duk da cewa zuwa da wuri yafi da wurwuri.

Shin Buhari na kaunar talakan Arewa ne, yayin da yayan talakawa musamman ma na Katsina, Zamfara, Kaduna su ka koma daji suka zama yan ta’adda, wanda a baya sune na gaba-gaban sai Buhari.

Allah ya kiyaye gaba.

alhajilallah@gmail.com

Tags: AbujaBuhariLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Martabar Najeriya na ta zubewa a Afrika saboda rashin tsayayyun shugabanni – Obasanjo

Next Post

RADDIN GWAMNONI GA GWAMNATIN BUHARI: Kasa magance matsalar tsaro da kasa cika alƙawurran da Buhari ya yi ne su ka haifar da talauci a karkara

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
RADDIN GWAMNONI GA GWAMNATIN BUHARI: Kasa magance matsalar tsaro da kasa cika alƙawurran da Buhari ya yi ne su ka haifar da talauci a karkara

RADDIN GWAMNONI GA GWAMNATIN BUHARI: Kasa magance matsalar tsaro da kasa cika alƙawurran da Buhari ya yi ne su ka haifar da talauci a karkara

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHUGABANCIN APC: Ko biyayyar da Ganduje ke wa Tinubu za ta sa ya yi kargo a ɗigirgiren shugabancin APC?
  • SAKAMAKON AMBALIYA: Yadda yunwa ke nuƙurƙusa da kisan talakawa a yankunan Arewa
  • ‘Kwankwaso ne ya kada mu a shari’ar Kano saboda kwaɗayin kujerar minista a gwamnatin APC – Abbas Akande
  • ‘Gazawar Najeriya gazawar jinsin baƙar fata ne na duniya baki ɗaya’ – Shettima
  • Kotun Amurka ta amince Jami’ar Jihar Chicago na iya jinkirta sakin bayanan karatun Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.