Zaben 2023 zai bambanta da za6en 2015 da 2019. A za6en 2015, gwagwarmayar samar da shugaban kasa ne tsakanin Kudanci da Arewacin Najeriya. Goodluck d’an kudu yana son komawa mulki, Buhari d’an Arewa yana so ya kar6e kujerar. Wannan ba sabon abu bane a siyasar Najeriya. A za6en 2019 kuma, ‘yan Arewa ne su ke neman kujerar shugaban kasa. Fad’an cikin gida ne.
Bayan jami’yyar APC ta cigaba da mulki tun daga lokacin da ta kwace kujera a hannun PDP, wasu su na ganin an cigaba. Wasu kuma su na ganin gwara ma lokacin da PDP d’in take mulki. Tun a za6en 2019 wasu su ka koma zawarcin tsohuwar jami’ya mai mulki. Shiyasa alqaluman zaben 2019 su ka bada mamaki saboda tazarar da Buhari ya bawa Atiku na jami’yyar PDP babu yawa sosai.
Atiku Abubakar tsohon d’an takarar shugaban kasa ne tun daga 1993 har zuwa yau. Shiyasa ya kasance barazana ga jami’yya mai mulki saboda yana da abunda ake kira da turanci da “Political structure”. Duk sanda lokacin siyasa ya zo saidai kawai ya yayyafa mata ruwa ya cigaba da yaqin neman za6ensa.
Gaskiyar lamari, tun bayan lokacin da ake zaton APC za ta bawa Tinubu takara, wasu su na gani kamar babbar dama ce ta cin za6e a wajen Atiku saboda za a iya yin siyasar 6angaranci. Talaka zai iya tsayawa a 6angarensa. Sannan babban abunda zai iya bawa PDP dama shine tsarin Musulmi-Musulmi da Tinubu ya d’auko. Hakan ma babbar dama ce ta mallakar kuri’un kiristocin Najeriya a ko ina kamar yadda tsohon sakataren gwamnatin tarraya, Babachir Lawal, yace, “Sai mahaukaci a cikin kiristoci ne zai za6i Tinubu akan tsarin Musulmi-Musulumi.”
Saidai ana wata ga wata, kuri’un Atiku na Arewa za su iya samun barazana a wajen d’an takarar sabuwar jami’yyar NNPP, Rabi’u Musa Kwankwaso. Dama a inda za a iya yiwa APC barazana sosai shine Arewacin Najeriya.
To yanzu barazanar ta koma tsakanin Atiku da Kwankwaso. A can Kudancin na Najeriya kuma, Tinubu da Peter Obi ne za su fafata akan kuri’un ‘yan kudu. Amma abun tambaya a nan shine, can sun kai ‘yan arewa yawa?
Gaskiya komai zai iya faruwa a zabe mai zuwa. Duk mai nazarin siyasa zai iya kallon wasu abubuwa. Wasu talakawan su na neman canji. A yayin da wasu su ke gani kamar idan aka kuma za6ar APC za a ji dad’i a gaba. Wasu kuma su na gani kamar Kwankwaso da Peter Obi ba za su iya cin za6e ba saboda yanzu su ka fara tasu tafiyar.
Wasu kuma su na gani kawai wasan sai an tashi. Koma dai menene, akwatin za6e ce kawai za ta tantance.
Allah ya sa mu ga alheri.
Discussion about this post