A karon farko a tarihi, Gwamantin Jihar Abiya ta kafa dokar raba gadon da mahaifi, mahaifiya ko mijin aure ya mutu ya bari tare da mata.
Gwamnan Jihar Abiya Okezie Ikpeazu ne ya bayyana cewa ya sanya wa dokar hannu, kamar yadda Kakakin Yaɗa Labaran Gwamna, mai suna Onuebuchi Ememanka ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Laraba.
A ranar 16 Ga Nuwamba ne dai Majalisar Dokokin Jihar Abiya ta amince da dokar, wadda tun farko ƙudiri ce wanda Kakakin Majalisar Abiya, Chinedu Orji ya gabatar, kuma aka amince ta zama doka.
Gwamna Ikpeazu ya ce lokaci ya yi da za a daina nuna bambanci tsakanin mace da namiji, kuma gwamnatin sa ba za ta maida mata a matsayin jinsin da ke ƙasa da maza ba.
Ikpeazu ya buƙaci a yi watsi da tsohuwar al’adar tauye wa mata haƙƙi, a riƙa ba su duk wani haƙƙin da ya wajaba a riƙa ba su.
Idan ba a manta ba, cikin 2020 ne Kotun Ƙolin Najeriya ta haramta hana mata cin gadon da iyayen su ko mazan su su ka mutu su ka bari.
Kotun Ƙoli ta bayyana cewa ƙabilun da ke hana mata cin gadon iyaye ko mazan su, sun take Doka Sashe na 42(1) (a) da (2) na Kundin Dokokin Najeriya na 1999.
Gwamna Ikpeazu ya kuma jinjina wa Kakakin Majalisar Abiya, dangane da kawo wannan ƙudiri da ya yi a majalisa, har aka amince da shi ya zama doka.
A Najeriya akwai ƙabilu da dama waɗanda ba su raba gado da mata.
Musulunci dai ya wajibta raba gado da mata fiye da shekaru 1,400 da su ka gabata.
Discussion about this post