IKON ALLAH; Yanzu nake samun labarin wai tun safe ake can ana meeting a karamar hukuma ta Gaya, da masu ruwa da zaki domin a tursasa shugabannin jam’iyya na mazaba ta su kore ni daga jam’iyyar mu ta APC. Hilarious!
Ko laifin me nayi, oho?
Sai dai abin lura anan shi ne kamar duk wani dan jam’iyya da ya san me yake yi, ba ina cikin jam’iyyar APC ba ne ido a rufe, na san duk wasu hakkokin jam’iyya da yake kaina, haka kuma na san duk wasu hakkoki na dake kan jam’iyya da suke kunshe a cikin kundin tsarin mulkin jam’iyyar.
Idan akwai laifin da na yi wa jam’iyya da na cancanci a kore ni, to zan yi maraba da hakan.
A baya – bayan nan na ga wasu rubututtuka akan wasu suna neman jam’iyya ta hukunta ni saboda na ki zuwa taron kaddamar da takarar Gwamna a Gaya na tafi kallon World Cup a Qatar, rashin sani, na je Qatar ne a cikin tawagar da Nigeria ta tura, domin mutunta Sarkin Qatar, da ya aikowa Nigeria takadar gayyata duk kuwa da cewa ba mu yi nasarar shiga gasar ba. (It was an official trip.)
Idan kuma akan karar da na shigar ne, da nake kalubalentar zaben fidda dan takarar Majalisar Tarayya ne, wannan kuwa zan kara maimaita maganganu na baya ne “Ba zan janye karar da na shigar a kotu ba”, a matsayina na dan Nigeria, ina da hurumin zuwa kotu don bin hakkina a duk lokacin da nan gamsu da wani hukunci ko mu’amala ba, kuma kowa yana da wannan hurumi, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada, idan kuma hakan laifi ne da zai sa a kore ni a jam’iyya, to lalle ina tabbatar musu cewa hakan ba a cikin kudin tsarin jam’iyyar mu ta APC aka samo shi ba.
Ba zan yi doguwar magana ba a yanzu, zan jira sai lokacin da takardar korar tawa za ta iso hannuna, a lokacin ne zan samu damar yin maganganu na da hujja.
A karshe, a jam’iyyar APC kam, musamman a matakin kasa, muna da gurbi mai karfi, ko a yammacin nan ma sai da muka yi meeting na darektocin yakin neman zaben Asiwaju Bola Tinubu, gobe kuma idan Allah ya amince za mu ziyarci jihar Bayelsa domin Yakin neman zabe, a cikin sati mai zuwa kuma za mu dira a birnin London duk a cikin tafiyar Tinubu/Shettima.
Allah ya ci gaba da kare mana mutunci mu!
Discussion about this post