Yayin da jami’o’in Najeriya su ka shafe watanni bakwai a rufe cikin 2021, rahoton Ofishin Jakadancin Amurka da ke Najeriya ya tabbatar da cewa ɗalibai 14,438 ne su ka fice zuwa neman ilmi a manyan makarantun Amurka, a zangon karatu na 2021/2022.
Rahoton ya nuna cewa an samu ƙarin yawan ɗalibai da kashi 12.3% daga adadin ɗalibai 12,860 da su ka tafi karatu daga Najeriya zuwa Amurka.
Amurka ‘yan Najeriya su ka fi tafiya karatu, daga nan sai Birtaniya.
Rahoton ya ce a zangon 2019/2020 an samu mutum 914,095 waɗanda su ka je Amurka karatu daga ƙasashen duniya baki ɗaya.
Yayin da a zangon 2022 aka samu mutum 948,000 daga ƙasashen duniya baki ɗaya.
Rahoton ya kuma daddale cewa ‘yan Najeriya ne mafiya yawan zuwa Amurka karatu, inda ofishin jakadancin Amurka a Abuja ya nuna cewa kashi 33% na masu zuwa Amurka karatu daga Afrika, duk daga Najeriya su ke.
Haka nan rahoton ya ce tsawon shekaru goma a duk shekara a jere adadin ƙaruwa ya ke yi, ba raguwa ba.
Baya ga Amurka da Ingila, wasu ƙasashen da ‘yan Najeriya ke tafiya karatu, sun haɗa da Malysia, Canada da Indiya.
Discussion about this post