• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

MASU LAYYA SU NA HIDIMA DA NAMA: Kasafin Naira biliyan 7.2 na gyare-gyaren Fadar Shugaban Ƙasa sun yi kaɗan – Umar

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
November 4, 2022
in Rahotanni
0
Mun cika alƙawuran da muka ɗauka wa ƴan Najeriya – Buhari

Babban Sakataren Fadar Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa kasafin Naira biliyan 21.1 na fadar sun yi kaɗan matuƙa.

Tijjani Umar ya na magana ne dangane da Naira biliyan 7.2 daga cikin kuɗaɗen waɗanda za a kashe a ɓangaren gyare-gyare da kula da fadar.

Kasafin 2023 dai ya ware naira biliyan 21.1 domin kashewa a Fadar Shugaban Ƙasa.

A cikin kuɗaɗen za a kamfaci Naira biliyan biyu a sayo sabbin motoci sannan a kashe naira miliyan 644 wajen gyaran Karamin Ofishin Shugaban Ƙasa da ke Legas.

Najeriya za ta ciwo bashi na sama da tiriliyan 8 kuma za ta biya bashi na sama da tiriliyan 6 duk a cikin 2023.

Ƙasar na fama da matsalar tattalin arziki, ƙarancin kuɗaɗen shiga da kuma tsadar rayuwa.

Najeriya ta ƙara afkawa cikin wani mawuyacin halin da ake canja Dalar Amurka 1 kan Naira 900, alhali lokacin da Buhari ya hau mulki ba ta wuce Naira 200 ba.

Matsalolin Da Su Ka Dabaibaye Kasafin 2023:

Cikin watan Oktoba ne Majalisar Dattawa ta fara zaman nazarin Kasafin 2023 na naira tiriliyan 20.5, wanda Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar a ranar Juma’a.

Sanatocin da su ka yi magana da shawarwari a lokacin nazarin kasafin, sun nuna rashin amincewa da yadda Gwamnatin Tarayya za ta kashe har naira tiriliyan 8.2 kan ma’aikatan gwamnati da ayyukan yau da kullum na tafiyar da gwamnati. Amma kuma za a kashe naira tiriliyan 5.35 kacal wajen yi wa ‘yan Najeriya ayyukan raya ƙasa da su ka haɗa har da titina da sauran su.

A kasashin dai Gwamnatin Tarayya za ta ciwo bashin naira tiriliyan 8.27, kuma za ta biya bashin naira tiriliyan 6.31. Sannan kuma ma’aikatan gwamnati za su lashe naira tiriliyan 4.99.

SANATA NDUME: Wauta Ce A Ciwo Bashin Da Za A Kashe Kan Ma’aikatan Da Su Ne Kashi 1% Bisa 100% Na ‘Yan Najeriya:

Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa maganar gaskiya bai yiwuwa a ce Gwamnatin Tarayya za ta kashe naira tiriliyan 8.2 kan ma’aikatan gwamnatin tarayya, waɗanda yawan su bai wuce kashi ɗaya tal na yawan ‘yan Najeriya su miliyan 200 ba.

Ya ce kamata ya yi a ce kuɗin da gwamnati za ta yi wa sauran ‘yan Najeriya aiki ya fi yawan kuɗin da za ta kashe wa ma’aikata fintinkau.

“Amma ai hankali ma ba zai ɗauka ba, a ce wai za a ciwo bashin naira tiriliyan 8.27, kuma a kashe naira tiriliyan 8.2 kan ma’aikatan gwamnatin tarayya. Su kuma sauran ‘yan Najeriya a yi masu aikin naira tiriliyan 5.35 kaɗai.” Inji Ndume.

Daga nan sai ya yi kiran da a binciki yadda a duk shekara kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa kan ta ke ƙaruwa maimakon raguwa, duk kuwa da cewa a kullum fasahar zamani na rage ɗawainiyar kashe kuɗaɗe da kawo sauƙi wajen gudanar da ayyuka.

SANATA BETTY APIAFI: Asusun Gwamnati Na TSA Ya Na Yoyo, A Binciki Waɗanda Su Ka Ɓula Shi:

Sanata Betty Apiafi, wata ‘yar PDP daga Jihar Ribas, ta fallasa cewa akwai rahotannin da su ka tabbatar da cewa Asusun Bai Ɗaya na PDP ya na yoyo, don haka a jingine batun ciwo bashi tukunna, a dawo a yi binciken inda kuɗaɗen Najeriya ke zurarewa, kuma a gano masu tara buhuna su na jide kuɗaɗen.

Ta ce wahalar banza ce duk shekara a yi ta ciwo bashi, amma kuma an kashe toshe hanyoyin da ake kwashe kuɗaɗen ƙasar nan.

SANATA SMART ADEYEMI: Attajiran Da Su Ka Kimshe Kuɗaɗe A Bankuna Su Bai Wa Gwamnati Ramce:

Sanata Smart Adeyemi daga Jihar Kogi, ya bayar da shawarar cewa maimakon a riƙa fita ana ciwo bashi, ya kamata manyan attajiran da su ka kimshe kuɗaɗe a cikin bankuna kuma ba su taɓa kuɗaɗen, su riƙa bai wa gwamnati ramce.

“Akwai maƙudan kuɗaɗe har maƙudan dalolin da manyan ‘yan Najeriya su ka kimshe a bankuna, ba a taɓa su. Ya kamata su riƙa bai wa Najeriya ramce.”

Kaɗan kenan daga cikin waɗanda su ka yi maganganu masu yawa a yayin zaman.

SANATA AHMAD LAWAN: A Daƙile Ɓarayin Ɗanyen Mai Don A Rage Yawan Ciwo Bashi:

Sanata Lawan ya baje faifan yadda Najeriya za ta rage ciwo bashi da rage giɓin kuɗaɗen kasafi

Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya bayyana cewa matsawar Najeriya ba ta tashi tsaye ta daƙile barayin danyen mai da masu fasa bututu ba, to nan ba da daɗewa ba tattalin arzikin Najeriya zai iya durƙushewa.

Lawan ya yi wannan bayani lokacin da ya ke gabatar da jawabi kafin Shugaba Muhammadu Buhari ya fara jawabin gabatar da Kasafin 2023 na naira tiriliyan 20.52 a Majalisar Tarayya.

Lawan ya ce a yanzu ɓarayin ɗanyen mai su ne manyan abokan gabar Najeriya. “Ya kamata a tashi haiƙan a kakkaɓe wannan gagarimar matsalar ta ɓarayin ɗanyen mai, kafin su kai ga tarwatsawa ko durƙusar da tattalin arzikin Najeriya.”

Lawan ya ce idan aka magance gagarimar satar ɗanyen mai, to za a samu ƙarin kuɗaɗen shiga, kuma hakan zai rage ciwo bashi, tare da rage giɓin kasafin kuɗi.

Shawara ta biyu da Sanata Lawan ya bayar, ita ce “a sake nazarin ɗage biyan harajin shigo da wasu kaya da ake yi wa wasu mutane ko kamfanoni. Kuma a rage bai wa wasu kamfanoni iznin karɓar haraji a madadin gwamnatin tarayya ana biyan su lada.

“Kuma a rage bai wa wasu kamfanoni damar kashe kuɗi su na yin wasu ayyukan gwamnatin tarayya, daga baya su na karɓar haraji har sai sun karɓi kuɗin kwangilar su da ribar su tukunna.”

Lawan ya buga misali da cewa hukumomi ne irin su Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa, Hukumar NIMASA da Hukumar Sadarwa ta Kasa (NCC), duk kamata ya yi su riƙa karɓar harajin su da kan su, kamar yadda Hukumar Kwastan da Hukumar Tara Kuɗaɗen Harajin Cikin Gida (FIRS) ke Karɓar na su da kan su, ba wasu kamfanoni ke karɓar masu ba.

Lawan ya ce waɗannan duk hanyoyi ne na ƙarin kuɗaɗen shiga ga gwamnatin tarayya, waɗanda za su haifar da rage ciwo bashi don a cike giɓi a kasafin kuɗi.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin cewa Buhari ya ce Za a ciwo bashin naira tiriliyan 8:8, don a cike giɓin Kasafin 2023.

Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar Kasafin 2023 na naira tiriliyan 20:51, a gaban Majalisar Tarayya.

Kasafin wanda ya gabatar a ranar Juma’a, shi ne na takwas kuma na ƙarshe a mulkin sa da ya gabatar.

A cikin jawabin sa, Buhari ya bayyana cewa za a samu giɓi na naira tiriliyan 10.78, amma kuma za a cike giɓin da kuɗaɗen bashin da za a ciwo har naira tiriliyan 8.8.

Haka nan kuma ya ce a cikin kasafin, za a kashe naira tiriliyan 6.31 wajen biyan basussuka.

Ya bayyana cewa an tsara kasafin bisa kintacen cewa Gwamantin Tarayya za ta samu kuɗin shiga har naira tiriliyan 16.87 cikin 2023. Kuma ana sa ran a riƙa haƙo gangar ɗanyen mai miliyan 1.69 a kowace rana, yayin da aka yi kintacen cewa za a riƙa sayar da kowace ganga ɗaya kan Dalar Amurka 70.

Wannan kasafin wanda aka raɗa wa suna Kasafin Rage Giɓi Da Rage Ciwo Bashi, ya nuna bai ci sunan sa ba, domin za a ciwo har naira tiriliyan 8.80 a matsayin bashi cikin 2023.

Yayin jawabin sa, Buhari ya yi bitar ayyukan da gwamnatin sa ta gudanar cikin shekaru bakwai da kuma bibiyar yadda aka kashe kuɗaɗen kasafin 2022.

Tags: BewsBuhariHausaKasafin KuɗiLabaraiPREMIUM TIMES
Previous Post

Ku Guji Auren Dole Domin Zaman Lafiyar Al’ummah! Daga Imam Murtadha Gusau

Next Post

MATSALAR MULKIN BUHARI: Ana yin ƙarin gishiri a labaran tulin bashi da taɓarɓarewar tattalin arzikin – Hadimin Buhari

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Gwamnatin Buhari ta bada kwangiloli 878 daga 2015 zuwa 2021 -Boss Mustapha

MATSALAR MULKIN BUHARI: Ana yin ƙarin gishiri a labaran tulin bashi da taɓarɓarewar tattalin arzikin - Hadimin Buhari

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kotun Amurka ta amince Jami’ar Jihar Chicago na iya jinkirta sakin bayanan karatun Tinubu
  • JAMI’AR GUSAU: Ba tun yau bane ƴan ta’adda ke yi wa ɗaliban jami’ar ɗauki ɗaiɗai
  • ƘALUBALE GA MATAWALLE DA BADARU: Sace Ɗaliban Jami’ar Gusau da Dawowar Ta’addanci a Arewa Maso Yamma, Daga Ahmed Ilallah
  • Wike ya soke lasisin mallakar filayen wasu jigajigan Najeriya ciki har da Peter Obi
  • Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.