Ɗaya daga cikin nasarorin da gwamnatin gwamna Nasir El-Rufai za ta yi alfahari da shi a tsawon mulkin ta a jihar Kaduna shine naɗa gogaggen ɗan jarida, wanda ya rikiɗa ya zama gogaggen masanin harkar tsaro Kwamishinan tsaro a jihar.
Ba wani bane kuwa illa sannanen matashi, haziki kuma gogarman tabbatar da ana zaman lafiya a jihar Kaduna, Honarabul Samuel Aruwan.
Samuel Aruwan ya fara aiki a gwamnatin gwamna El-Rufai ne a matsayin mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, daga bisani kuma bayan nasarar da gwamnatin ta samu a 2019, sai hazaƙarsa ya sa gwamna El-Rufai ya ga yafi cancanta ya zama kwamishinan tsaron jihar.
Wasu da dama sun yi tambayar yaya aka yi gogarman ɗan jarida ya koma harkar tsaro dare ɗaya? Amsar kuwa ita ce, tun bayan naɗa Aruwa Hadimin gwamna, El-Rufai, da yake mutum ne mai hangen nesa ya hango irin baiwar da Allah yayi wa Samuel Aruwan. Daga wannan lokacin ya rika saka shi a hanya, yana nuna masa sannan ya na saka shi yin ayyukan tsaro na jihar tare da manyan hukumomi da jami’an tsaron jihar Kaduna.
Da yake faɗuwa ce ta zo daidai da zama kafin wani ɗan lokaci Aruwan ya zama karfen kafa, ya goge, ya zama abin alfahari ga gwamna da mutanen jihar Kaduna, wanda ake misaltawa cewa da za asamu irin sa 10 a kasar nan da ba haka ba, musamman a harkar tsara tafiyar yadda za a shawo kan matsalar tsaro a kasar nan.
Wani abu da ya sa dole ka yi jinjina da yabo ga Aruwan a wajen aikin sa shine yadda akida ta siyasa, addini, Kabilanci ko kuma bangaranci ba su cikin tafiyarsa ko kaɗan. Idan aiki ya zo, aiki kawai ya ke yi, ya tsage gaskiya komai ɗacin ta sannan kuma ya yi abinda ya kamata.
A cikin wasu ɗabi’un sa na kirki da suka fito waje ƙarara sun haɗa da tausayi da sanin ya kamata. Ba sau ɗaya ba, Aruwan ya kan zarce gaba da kansa tare da jami’an tsaro su tunkari wuraren da aka samu tashin hankali ko matsala ta tsaro a jihar domin kawo karshen matsalar cikin gaggawa.
Ba a cikin garin Kaduna ba, Aruwan ya sha ya tunkari babban titin Kaduna-Abuja a duk lokacin da aka samu matsala da suka haɗa da ko dai cunkoso da toshewar hanya ko kuma matsalar harin ƴan bindiga.
Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya na yaba masa da jinjina masa bisa kokari da jajircewa da yake yi a aikin sa. Sannan kuma duk bayan watanni hudu yakan gayyaci manyan jami’an gwamnati da na tsaron jihar domin bayyana musu irin ayyukan da ma’aikatarsa ta tsaro ke yi a jihar ta hanyar bada bayanan kan yadda halin tsaro yake a jihar zuwa wannan lokaci.
Duka wannan suna halalen Samuel Aruwan da kuma kwarewa da yayi a aikin sa na kula da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna.
Discussion about this post