A farkon watan Satumba ne Yan Sanda a Jigawa suka kama Aliyu Husseini mai sana’ar tuka kwalekwale saboda da kifewa da kwale kwalensa tayi ta kashe akalla mutum takwas.
Amma dai daga bisani Yan Sandar sun saki Husseini ba tare da sun gurfanar da shi a gaban kotu ba. Husseini ya shaidawa wakilinmu a Jigawa cewa ya dawo bakin aikinsa yana daukar mutane a kwalekwalensa ba tare da ya saka ko kuma ya ajiye rigunan kariya ba wato (life jacket) tare da shi ba.
Mutanen garin Birnin Kudu a Jihar Jigawa na yin tafiya ta hanyar hawa Jirgin ruwa wato (kwalekwale) saboda ambaliyyar ruwa da ya karya gadar da ya hada garin da babbar birnin Jihar da kuma Jihar Kano.
Jaridar PREMIUM TIMES HAUSA ta rawaito yadda ruwan sama ya haddasa ambaliyya a Jigawa, ambaliyyar tayi sanadiyar mutuwar mutane sama da dari, ta kuma mamaye gonakai da hallaka dabbobi. Ambaliyyar ta kuma karya gadoji da hanyoyi da dam a garin Haya dake Gwaram.
Hakan ya tilasta wa mutane anfani da kwalekwale wajen tafiye tafiye. Amma matuka kwalekwalen suna deban fasinjoji fiye da kima, kuma ba tare da sun basu rigar kariya ba.
Malam Husseini ya shaidawa PREMIUM TIMES HAUSA cewa a rana daya yakanyi ciniki har na naira dubu Hamsin zuwa Talatin a daukar mutane a kwalekwalensa ya tsallaka dasu dalilin karyewar gada.
Ya ce yana aikin taimakawa mutane ne saboda gwamnatin ta Jigawa ta gaza kawowa mutanen dauki na gaggawa lokacin da gadar ta karye.
“Muna yin iya kokarinmu wajen taimakawa mutane. Ba don taimakawa da muke yi ba, da yanzu mutane sun shiga cikin mawuyacin hali, saboda babu hannun gwamnati anan. Muna bukatar taimakon gwamnati, babu wanda yake zuwa nan wajen sai Yan Jaridu da kuma Yan Sanda da suka zu sukayi kame a lokacin da kwalwkwalenmu ya kefe, cewar Husseini.
“Akalla mun sami gawarwarki sun kai ashirin a nan wanda ruwa ya kawosu daga wasu garuruwa. Mun binne wasu, wasu kuma mun baiwa masu shi, inji Husseini.
Husseini ya kara da cewa suna taimakawa marasa lafiya masu zuwa neman magani, kuma basu karbar kudi a wajen tsofaffi da kuma mutanen da suka dauko gawa.
Shi ma mai sana’ar kwalekwalen wanda ya taba yi a Legas, Ya’u Musa, ya shaidawa PREMIUM TIMES HAUSA cewa sana’ar tana da wuya a Jigawa saboda babu ka’ida, kowa yi yake yi batare da sanin gwamnati ba.
Ya ce a Jigawa suna daukar fasinjoji yadda suke so ba tare da rigar kariya ba. Amma a Legas sai anyi maka ka’ida kuma an baka rigar ruwa saboda gudun faruwar hatsari.
A garuruwan Ringim da Hadejia suma suna fama da ambaliyyar ruwan, an samu mace mecen mutane ta hanyar kefewar kwalekwale da kuma rugugewar gidaje.
A Ringim, garuruwa irinsu Dabi, Majiyawa, Dare, Gagarin, Yan-Dutse, Malamawar Yandutse, Cori, Gujaba, Sankara, Auramo da Garin Gada, suna cikin mawuyacin hali.
Surajo Ya’u wane wanda ya rasa mata, da yaro da kuma suruka ta hanyar kefewar KwaleKwale ya shaidawa PREMIUM TIMES HAUSA cewa wannan shi ne ambaliyya mafi mune a karamar Hukumar ta Ringim.
Malam Ya’u yace Matarsa mai suna Nasiba Muhammad, dansa mai suna Mahmud da kuma surukarsa mai suna Suwaiba Mustapha sun rasu ne bayan da jirkinsu na kwalekwale ya kefe akan hanyarsu ta zuwa ta’aziya daga garin Dabi zuwa Siyangu
Jaridar PREMIUM TIMES HAUSA tayi kokarin jin ta bakin shugaban Hukumar Aikin Jinkai na Jihar Jigawa wato (SEMA) Sani Yusuf, ta yadda za’a magance yawan hatsarin kwalekwale a Jigawa amma bamu Kai ga samunsa ba.
Discussion about this post