Mako ɗaya da fara kamfen na yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na PDP, wasu masu kiran kan su ‘Dattawan PDP Magoya Bayan Atiku’, sun yi tattaki har gidan sa a Abuja, su ka kai masa takardar ƙorafin cewa ya gaggauta sauya Babban Kwamandan Yaƙin neman zaɓe da kuma wasu Baraden Yaƙin kamfen ɗin.
A cikin wasiƙar, sun bayyana cewa akwai buƙatar yi wa Rundunar Yaƙin Shugaban Ƙasa ta Atiku Abubakar (PCC) garambawul, domin a kauce wa sake maimaita babban kuskuren da aka yi a yaƙin neman zaɓen 2019, inda Darakta Janar na yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar, wato Gbenga Daniel ya fice ya koma wata jam’iyyar ana tsakiyar yaƙi.
A kan haka ne dattawan ke roƙon a gaggauta naɗa Raymond Dokpesi ya jagoranci rundunar yaƙin ta Atiku 2023.
Sun bayyana cewa Dokpesi ya fi cancanta, domin ya yi a n gani sosai a 2019, kuma ya nuna tsananin kishin jam’iyya da kishin ɗan takarar ta.
Shugaban ƙungiyar fattawan mai suna Lawrence Okojie ne da Sakatare na Ƙasa Peters su ka sa wa takardar hannu.
Cikin waɗanda su ka yi wa manema,labarai jawabi bayan sun miƙa koken su a gidan Atiku, har da Shugabar Reshen Mata na dattawan, Deborah Makinwa.
Sun ce a cikin Mataimakan Daraktoci akwai waɗanda kishin jam’iyyar da kuma jajircewar su bai kai har cikin zuciyar su ba.
Don haka su ka nemi a ƙyale kowane darakta ya naɗa mataimakin da ya gamsu da aikin sa.
Wannan ƙorafi ya zo ne kwana biyu bayan Sanata Ken Nnamani ya ce ganganci ne ya sa PDP ta fara kamfen ba tare da gwamnonin ta biyar ba.
Tsohon Gwamnan Jihar Enugu, kuma Sanata a yanzu, Ken Nnamani, ya ce babban kuskure ne da ganganci da har jam’iyyar PDP ta fara kamfen ɗin zaɓen shugaban ƙasa, ba tare da gwamnonin jam’iyyar biyar daga kudu ba.
Nnamani ya bayyana haka cikin wata sanarwar da ya aiko wa PREMIUM TIMES a ranar Talata.
Ya ce kwata-kwata ba daidai ba ne, kuma kasada ce babba a ce PDP ta fara yaƙin neman zaɓen ta a kudu, Jihar Akwa Ibom, ba tare da gwamnonin kudu biyar da ke cikin jam’iyyar ba.
Ya ce bai ga yadda za a yi nasara ba, idan gwamnonin biyar su ka ƙi bayar da haɗin kai lokacin zaɓe a jihohin su.
Ya ce ko an ƙi, ko an so gwamnonin jagorori ne a jihar su, kuma su ne kusa da jama’ar karkara ba ‘yan siyasar Abuja ba.
“Shi ɗan siyasar Abuja aikin shi kaɗai ya baza babbar riga ya shirya taron gangami, daga ranar kuma ba a ƙara ganin shi a jihar. Gwamna shi ne mai jama’a. Don haka idan ka wulaƙanta gwamna, to tamkar ka haɗa ne har da na ƙarƙashin sa duk ka wulaƙanta su.”
PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin cewa Jirgin yaƙin PDP na tangal-talgal, saboda gwamnoni biyar sun ƙi hawa a yi lodin kamfen tare da su.
Duk da cewa jam’iyyar PDP ta ƙaddamar da kamfen ɗin yaƙin neman zaɓen 2023 a Akwa Ibom cikin nasarar tara ɗimbin jama’a, ƙaurace wa gangamin da gwamnoni biyar su ka yi ya nuna har yanzu akwai jan-aiki ga Atiku sosai kafin ya dangana da kujerar shugaban ƙasa.
Gwamnonin guda biyar da ba su halarci taron ba, sun haɗa da Nyesom Wike na Jihar Ribas, Seye Makinde na Jihar Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu, Ikpeazu Okozie na Abiya sai kuma Samuel Ortom na Jihar Benuwai.
Su huɗun su na goyon bayan Wike ne, wanda ya jagorance su bijire wa PDP bayan an tsayar da Atiku takarar shugaban ƙasa.
Su biyar ɗin dai su na neman tilas sai shugaban PDP, Iyorchia Ayu ya sauka a naɗa ɗan Kudu, domin a tabbatar da adalci a shugabancin PDP.
Gangamin wanda PDP ta yi a Filin Wasa na Godswill Akpabio International Stadium, ya cika fal da magoya bayan PDP, inda a wurin Atiku ya sha alwashin cewa idan aka zaɓe shi, to za a yi bankwana da talauci da matsalar tsaro da rashin aikin yi a Najeriya.
Idan ba a manta ba, waɗannan gwamnoni biyar ba su halarci taron ƙaddamar da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na PDP ba.
Masu bibiyar lamarin siyasa na ganin cewa PDP za ta iya fuskantar matsala matsawar ba ta sasanta da gwamnonin biyar ba.
Su Wike dai su na jin haushin yadda ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da kuma Shugaban PDP Iyorchia Ayu duk su ka fito daga yankin Arewa.
PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin da rundunar yaƙin Bola Tinubu na APC ta ce, rikicin da hasalallun gwamnonin PDP ke yi da shugabannin jam’iyyar su, alheri ne ga APC.
Rundunar Yaƙin Tinubu 2023 ta ce turnuƙun rikicin da wasu hasalallun gwamnonin PDP ke yi da shugabannin jam’iyyar su, alheri ne ga jam’iyyar APC.
CIkin wata sanarwa da ɗaya daga cikin Kakakin Yaɗa Labaran Rundunar Tinubu, Festus Keyamo ya fitar a ranar Asabar, ya ce rikicin da ke faruwa a cikin PDP ya nuna cewa jam’iyyar ba za ta iya riƙe mulkin Najeriya ba, tunda har yau ta kasa ma sasanta rikicin da ke cikin gidan ta.
Keyamo ya ce PDP ba za ta iya haɗa kan Najeriya ba, tunda ta kasa haɗa kan iyayen jam’iyyar PDP ɗin.
Hasalallun gwamnonin dai bisa jagorancin Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas, har yau sun ƙi goyon bayan takarar shugabancin ƙasa da Atiku Abubakar ke yi, bisa dalilin cewa babu adalci wajen raba muƙaman jam”iyyar, saboda an damƙa shugabancin PDP ga ‘yan Arewa, inda kuma a yankin ne ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya fito.
Gwamnonin dai sun gindaya cewa kafin su fara goyon bayan Atiku, tilas sai Shugaban PDP, Iyorchia Ayu ya sauka an naɗa ɗan Kudu, domin a yi adalci.
Sannan kuma zargin da Wike ya yi wa Ayu kwanan nan, cewa ya raba wa shugabannin jam’iyyar cin hanci, kuma ya karɓi naira biliyan 1 a hannun wani a Legas, ya ƙara jefa PDP cikin ruɗani.
Keyamo ya ce har yau jam”iyyar PDP ba ta tuba daga ɗabi’ar ta na wawurar kuɗaɗe ba. Don haka ba za ta yaudari ‘yan Najeriya ba a zaɓen 2023.
“Ai mu rikicin da wasu gwamnonin PDP ke yi da shugabannin jam’iyyar su, alheri ne a gare mu. Sun kasa haɗa kan su, kuma rikicin wuru-wurun kuɗaɗe ya ƙara dagula PDP. Hakan ya nuna har yau ba su tuba daga ɗabi’ar su ta sata ba.
Keyamo ya ƙara caccakar PDP cewa sun bi son ran Atiku, sun ƙi bai wa Kudu takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, kamar yadda su ka yi yarjejeniya a baya.
Discussion about this post