Cikin wata tattaunawa da mai ban-tausayi, cike da damuwa ƙuncin rayuwa, Sani Giɗe ya shaida wa wakilin mu yadda a halin ‘yanzu ‘yar sa Farida Sani ke hannun gogarman ‘yan bindiga Dogo Giɗe, a matsayin amaryar sa da ya yi wa auren-dole, bayan sun kai hari a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yauri, ranar 17 Ga Yuni, 2021.
Idan ba a manta ba, a farmakin dai an kwashi ɗalibai 90 da kuma malamai. Amma an riƙa ceto wasu, daga baya kuma an riƙa tattaunawa da Gwamnatin Jihar Kebbi ana sakin wasu da kaɗan-kaɗan.
Zuwa cikin watan Janairu lokacin da aka saki ƙarin ɗalibai 30, saura ‘yan mata 11 ne su ka rage wurin su Dogo Giɗe, waɗanda ya tabbatar da cewa sun raba su a tsakanin su ‘yan bindigar, sun aurad da su, saboda Gwamnati ta ƙi biyan su kuɗin fansar da su ka nemi a biya su.
Sani Kaoje shi ne mahaifin ɗaya daga cikin ɗalibai mata da su Gogarma Dogo Giɗe su ka aura. Ya shaida wa PREMIUM TIMES irin yadda ya riƙa waya da Dogo Giɗe sau tarin yawa dangane da ‘yar sa da har yanzu ke hannun sa, a matsayin amaryar sa.
“Ina da ‘ya’ya 19 kuma mata na uku. Farida ita ce ta 15, kuma yanzu shekarun ta 16. Wato kenan ta na da shekaru 15 aka yi garkuwa da ita” Inji Sani Kaoje.
Ya shaida cewa sau da yawa Dogo Giɗe na kiran sa ya na nuna masa cewa tun da ba za a biya su naira miliyan da babura 30 da su ka nema ba, to za su auri yaran.
“Na sha yin waya da shi. Saboda ya na kira na sosai. Har dai ta kai ya nuna min cewa sun auri yaran. Bai fito ya nuna min cewa shi ya auri Farida ‘ya ta mai shekaru 15 a lokacin da aka kama ta ba. Amma sai ya karkatar da maganar ya ce min ta na hannun sa, shi ke kula da ita. Amma daga ƙarshe ya ce min matar sa ce, kuma ko ya mutu, a cikin gidan su akwai wanda zai gaje ta.”
Kaoje ya ce tabbas ya na yin waya da ‘yar sa Farida ba sau ɗaya ko sau biyu ba. Amma dai Dogo Giɗe ɗin ne ke kiran sa a waya, sai ya haɗa su su gaisa.
“Akwai ranar da ya haɗa da ita mu ka yi waya, ta kira ni ta ce min Baba akwai fa matsala, saboda za su aurad da mu.” Ni kuma dama ya rigaya ya shaida min haka.
Sani Yauri ya nuna gazawar Ministan Harkokin Ilmi Adamu Adamu, wanda ya ce bai yi komai ba, duk kuwa da cewa makarantar da aka sace yaran ta Gwamnatin Tarayya ce.
Sannan kuma ya shaida wa wakilin mu cewa Dogo Giɗe ya ce shi Gwamnati ya ke so ta sasanta da su, ba iyayen yaran ba.
“Dogo Giɗe ya ce min tun su na neman a biya su fansar naira miliyan 100, su ka rage su ka ce a biya naira miliyan 50 da babura 30, amma gwamnati ta yi banza da su. Wai shi ya sa su ka yanke shawarar aurar da sauran ‘yan matan da su ka rage a hannun su.” Inji Sani Yauri, wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne daya yi ritaya.
A ƙarshe ya nuna irin halin ƙuncin da su ke ciki, tun daga ranar da aka yi garkuwa da ‘ya’yan su har yau ɗin nan.
“Wasu iyayen masun mutu saboda takaici. Akwai kuma mahaifin wata ƙawar ‘ya ta mai suna Rebecca. To mahaifin ta ya shiga damuwar da ba ya iya hasala komai a rayuwa. Ko kuɗi ka miƙa masa, ba zai iya ƙidaya su ba.”
Discussion about this post