Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta nesanta kan ta daga wani ma’aikacin ta wanda ya yi rantsuwar shaidar ‘affidavit’ a kotu, dangane da rigimar zaɓen fidda-gwanin Sanatan Yobe ta Tsakiya.
Cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran INEC, Festus Okoye ya fitar a ranar Alhamis a Abuja, ya bayyana cewa hukumar ba ta umarci jami’in na ta da yin rubutacciyar rantsuwar a kotu ba a Babbar Kotun Tarayya ta Jihar Yobe da ke Damaturu.
Tsawon wata ɗaya kenan ana tabka rikici kan shin wane ne halastaccen ɗan takarar Sanatan APC na Yobe ta Arewa, tsakanin Bashir Machina da Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan
An zaɓi Machina a zaɓen fidda-gwani wanda aka gudanar a kan idon INEC, amma abin ɗaure kai, sai APC ta tura sunan Ahmad Lawan, maimakon na Machina tun a cikin watan Yuni.
A lokacin da aka gudanar za zaɓen, Lawan bai shiga takarar sanata ba, ya na can ya na fafutikar takarar zaɓen fidda-gwanin shugaban ƙasa na APC, wanda Tinubu ya yi nasara.
Ita kuma INEC ta ƙi amincewa da matsayar da APC ta ɗauka na tura mata sunan Lawan, wanda bai ma shiga takara ba a lokacin zaɓen fidda-gwani
Dama kuma jami’an INEC da su ka halarci taron sun bayyana Machina a matsayin wanda ya yi nasarar lashe zaɓen.
A ranar Laraba kuma PREMIUM TIMES ta buga labarin cewa wani ma’aikacin INEC a Jihar Yobe ya garzaya kotu ya shigar da ƙorafin yin jayayya da matsayar INEC ɗin.
Dama kuma wata ƙungiya mai suna TMG ta nuna tababar ko INEC za ta gudanar da zaɓe mai adalci a 2023.
A kotun, ma’aikacin INEC ɗin da bai ambaci sunan sa ba ya ce kada a yi la’akari da zaɓen Machina, domin a ranar zaɓen da ake cewa an yi masa, an yi wani zaɓen a mazaɓar Lawan, inda aka zaɓi Lawan ɗin.
Shi dai Kakakin INEC ya ce ya garzaya kotun don ƙasshin kan sa kawai.
Sai dai bai ambaci sunan sa ba, kuma bai faɗi ɓangaren da ya ke aiki a ofishin INEC ɗin ba.
Discussion about this post