Najeriya na daga cikin kasashen duniya dake yawan tura ƴaƴan su kasashen waje domin karaun jami’a. Ana kashe maƙudan kuɗade wajen biyan kudin makaranta da kudaden da ɗakibi zai yi amfani da su wajen tafiyar da al’amurorinsa na yau da kullum.
Wasu daga cikinsu kin dalilan da ya sa masu hali kan tura ƴaƴan su kasashen waje karatu sun haɗa da yajin aiki da malaman jami’o’i kan yi akai akai da kuma rashin samun karantarwa irin ta zamani da ake yi kamar yadda ake samu a wasu kasashen duniya.
Wannan yana daga cikin dalilan da yasa Farfesa Adamu Gwarzo ya kafa jami’ar Maryam Abacha dake Maradi, kasar Nijar da takwaranta sabuwar jam’iyyar Maryam Abacha dake Kano.
Jami’ar Maryam Abacha ta zamo tozalin ƴan Arewa musamman Arewa maso yammacin Najeriya.
Jami’ar Maryan Abacha ta zama abar yabo ga kowani ɗan Arewa da ma Najeriya baki ɗaya.
Tun bayan da aka kafa ta, sannan aka wanke sabbin dalibai jami’ar ta ke samun yabo daga ciki da wajen Najeriya.
A cikin kwanaki 30 da suka wuce, manyan ƴan Najeriya da suka hada da tsohon mataimakin shugaban Kasar Najeriya, Ariku Abubakar duk sun ziyarci jami’ar domin ziyarar gani wa ifo da kuma jinjina wa shugaban jami’ar Farfesa Adamu Gwarzo.
Baya ga shi, Ministan Sadarwa, Farfesa Ali Pantami sa mai martana sarkin Kano, aAminu Ado Bayero duk sun ziyarci ginin jami’ar domin nuna farincikin su da kuma jinjina wa Farfesa Gwarzo bisa wannan kokari da yayi na kafa jami’a mai kama da ta kasashen Turai da Amurka a Kano, Najeriya.
Farfesa Gwarzo mutum ne mai kishin al’ummarsa sannan kuma mai kishin su zamanto masu Ilimi. Baya ga kafa jami’o’i biyu da yayi ɗaya a Najeriya ɗaya a kasar Nijar, Farfesa Gwarzo na kan gaba wajen tallafawa har da manyan makarantun mallakin gwamnati tarayya da na jihohi a kasar nan har da ma wasu masu zama na kansu.
Ba a harka makarantu kawai ya tsaya ba, Farfesa Gwarzo ya baiwa ɗalibai dubbai tallafin samun ilimi kyauta a jami’ar Maryam Abacha baya ga taimako da yake yi wa mutane ɗaya bayan ɗaya a kowani lokaci idan hakan ya taso domin cigaban al’umma.
Abin alfahari ne ga mutanen yankin Arewa ace yau akwai mutum kamar Farfesa Gwarzo wanda ya kudiri aniyar sai ya kauda jahilci a cikin al’umma ya wanzar da ilimi kowa ya samu ya karu.
Fatan mu shine Allah ya karamsa basira da kuma hangen nesa ya kuma yi masa jagora da sanar mana da irinshi masu yawa a yankin Najeriya.
Discussion about this post