• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

MOHAMMED IDRIS MALAGI: Ɗan Siyasa Nagari, Mai Kishin Siyasar Ci Gaban Jama’a, Daga Jibrin Baba Ndace

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
September 20, 2022
in Ra'ayi
0
MOHAMMED IDRIS MALAGI: Ɗan Siyasa Nagari, Mai Kishin Siyasar Ci Gaban Jama’a, Daga Jibrin Baba Ndace

“Ba a kula masu kushe da hassada, Ba a yin la’akari da mai ƙoƙarin nuna gazawar mai ƙarfi,

Ko kuma masu ganin akwai inda mai yi masu ayyukan alheri ya kamata a ce ya fi haka ƙoƙartawa…”

-Theodore Roosevelt, tsohon shugaban Amurka

An shafe shekaru masu yawa, tun ma kafin samun ‘yancin Nijeriya, fitattun ‘yan jarida da mawallafa su na taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar ƙasar nan. Sun tsunduma siyasa ne baya ga ayyukan sadaukarwar da su ka riƙa wa jama’a a gidajen jaridu. A duniya ma masu kafafen yaɗa labarai sun zama mashahuran shugabanni da manyan ‘yan siyasa.

Kafin ma a samu ‘yanci kafafen yaɗa labarai sun kasance masu bayar da gagarimar gudummawar neman ‘yanci. Kuma masu kafafen yaɗa labaran nan da ‘yan jaridu sun yi rawar gani sosai a manyan muƙaman siyasa. Kafin samun ‘yanci an samu bayyanar manyan masu damawa a harkokin jarida sun zama mashahuran ‘yan siyasa. Wato Sa Herbert Macaulay da Dakta Nnamdi Azikwe, wanda shi ne ya zama Shugaban Ƙasa na farko a ranar da Nijeriya ta samu ‘yanci, 1 ga Oktoba, 1960.

Fitattun ‘yan jarida da masu gidajen jaridu sun ci gaba da kutsawa cikin harkokin siyasa, tun daga wancan lokacin har zuwa yau, inda a Jamhuriya ta biyu aka samu biyu daga cikin su su yi nasarar zama gwamna. Cif Lateef Jakande ya zama Gwamnan Jihar Legas, shi kuma Segun Osoba ya zama Gwamnan Jihar Ogun.

Waɗansun su kuma da dama sun riƙe muƙamai daban-daban, tun daga ‘yan majalisa, ciyamomi da kansiloli, ko kuma shugabancin wasu hukumomi da cibiyoyi.

Cikin Oktoba 2019, mawallafin jaridun Blueprint da Manhaja, Alhaji Mohammed Idris Malagi, ya yanke shawarar shiga wancan daji na siyasa da manyan ‘yan jaridu da mawallafa su ka keta. Da ya shiga kuwa, ya fito gadan-gadan neman muƙamin siyasa.

Tun daga wancan lokaci ne kuwa tafiya mai nisan zangon watanni 31 ana tuntuɓar jama’a, ganawa, kamun-ƙafa da tattauna yadda za a kai ga cimma nasara.

Lokacin da Malagi ya fito, wasu mutane sun riƙa cewa ya dai fito kawai don ya tayar-da-ƙura. Wasu ma cewa su ke yi wasa ya ke yi kawai. Akwai kuma masu yi masa kallon mutumin da ya yi samun kuɗin da ake cewa ‘dare-ɗaya-Allah-kan-yi-Bature’, wanda ya rasa yadda kai kashe kuɗaɗen sa, ya shiga siyasa kawai don ya yi ɓarusa.

Akwai wasu da su ka riƙa yi masa kallon sabon-yanka-rake ne a siyasa, wanda a ganin su, bai isa ya yi gasa da tsoffin ‘yan alewar siyasa ba.

Dukkan waɗanda su ka riƙa tofa albarkacin bakin su dangane da shigar Malagi siyasa, sun yi tsammanin da ya fara, za a neme shi a rasa, wato zai yi tashin kumfar gishirin Andurus. Sun yi tsammanin ya shiga ne kawai don neman suna.

Dama haka aka riƙa yi masa irin wannan mummunar fassara, lokacin da ya fara wallafa jaridar Blueprint. Saboda ya shiga harkar da ƙarfin sa, har ya girgiza waɗanda su ka fara yi masa kallon raini a lokacin. To irin haka lamarin ya maimaita kan sa, lokacin da ya shiga siyasa, inda manyan masu ruwa da tsaki da masu ganin sai irin su wane da wane ke iya yin gwamna a Jihar Neja, su ka riƙa yi masa kallon sabon-shiga.

Malagi ya shafe watanni 30 ana gwagwagwa da shi, inda ya jajirce, ya nuna cewa shi fa ya kawo ƙarfi, don haka ya fi wane ya girme ni.

Daga lokacin da ya fara zuwa lokacin da ya fara shiga cikin zukatan jama’ar sa, Alhaji Mohammed Idris ya shimfiɗa hajar siyasar sa a farfajiyar Jihar Neja, inda ya riƙa shelar siyasar da babu tashe-tashen hankula, a gefe ɗaya kuma ya na kutsawa garuruwa da lunguna ya jaddada kamfen a bisa batutuwan da su ka shafi ci gaban jiha da al’ummar ta baki ɗaya.

Yayin da sauran ‘yan siyasa su ka maida hankali su na yarfe da bankaura ta hanyar amfani da soshiyal midiya, su ka riƙa raba kawunan jama’a, shi kuwa Alhaji Mohammed Idris Malagi ci gaba ya yi da yi wa jama’a albishir da muhimmancin haɗin kai domin a gina ƙasaitacciyar Jihar Neja.

Cikin wannan lokacin ya gana da masu ruwa da tsaki na kowace shiyya a jihar. Dalilin haka abin koyi hatta ga su kan su abokan adawar siyasa, waɗanda kafin shigar Malagi siyasa ba su iya zama inuwa ɗaya.

Malagi ya riƙa kai wa dattawan jiha ziyara, su da sarakunan gargajiya, shugabannin addinai da jagororin jama’ar yankunan karkara. Kuma ya jawo matasa, dattawa da maza da mata. Sannan ya riƙa yin la’akari sosai da masu ruwa da tsakin APC mai mulki a Jihar Neja.

Mohammed Idris ya yi amfani da kuɗaɗen sa, lokacin sa da tsarin tafiyar sa har ya yi nasarar ratsa zukatan ‘yan jam’iyyar APC reshen Jihar Neja. Ya taka rawa sosai wajen bai wa jam’iyyar gudummawa. Akwai lokacin da ya bayar da gudunmawar motoci 31 da naira miliyan 43.

Lokacin da ya ke yankar tikitin takarar gwamna, Malagi wanda a yanzu shi ne Kakaaki Nupe, ya nanata babban dalilin da na neman tsayawa takarar gwamna.

“Niyya ta domin ganin na ciyar da Jihar Neja gaba ta bunƙasa a fili ta ke. Idan na zama gwamna zan yi aiki tuƙuru, tun daga sa’ar farkon shiga ta ofis domin na zaƙulo zarata kuma ƙwararru daga mazaje, mata, matasa, masu ilmi da marasa ilmi, manoma, masu sana’o’in hannu, ‘yan tireda da kowa da kowa domin su bayar da gudunmawar da za su iya bayarwa.”

Tun daga lokacin da ya fara tuntuɓar jama’a, bai taɓa yarda zuciya ta ɗebe shi ya yi abin da ya saɓa wa kyawawan halaye da ɗabi’un sa ba.

Yayin da wasu ‘yan siyasar jihar su ka rungumi ‘yan daba, siyasar ƙiyayya, ramuwar-gayya da ɓata sunan abokin hamayya, shi kuwa Alhaji Mohammed Idris Malagi sai ya maida hankali wajen kamfen ɗin rashin tayar da hankula, haɗin kai da zaman lafiya. Sai da Malagi ya tuntuɓi dukkan ‘yan takarar gwamna a ƙarƙashin APC na Jihar Neja. Kuma irin wannan albishir ya riƙa yaɗawa a lokacin ganarwa sa ƙananan hukumomi da mazaɓun ‘yan majalisar tarayya na jiha.

A tafiye-tafiyen da ya yi tun daga Lapai zuwa Agaie, zuwa Bida, Kutigi da Borgu, har Kontagora da Minna, ya riƙa ganawa da sarakunan gargajiya, shugabannin karkara da ‘yan siyasa, bai taɓa yi wani furucin da zai harzuƙa wasu ko ya yi kalamin da zai rura wutar jituwa ba.

Kakaaki Nupe ya yi takara kuma an fafata da shi sosai. Lokacin da sakamakon zaɓen bai yi masa daɗi ba, tangarɗar rashin gudanar da zaɓen kamar yadda ƙa’ida ta gindiya bai hana shi fara taya murna ga wanda ya yi nasara ba. Ko bayan zaɓen fidda-gwanin an riƙa yi wa Malagi kallon da bai kamata ba a cikin jiga-jigan APC na jihar, amma ya dake tare da kai zuciya nesa.

Rashin nasarar da yi ba ta hana shi cika wa Kungiyar ‘Yan Jarida Reshen Jihar Neja (NUJ), alƙawarin motar da ya yi masu ba. A ziyarar godiya da su ka kai masa, ya ce shi ba shi da abokin gaba a ciki ko wajen siyasa.

Duk da an yi zaɓen fidda gwanin APC wanda aka yi hasashen shi ne zai yi nasara, amma hakan bai yiwu ba, a fili dai ta tabbata cewa bai yi nasara ba, amma kuma ya samu galabar riƙe alakar siyasa. Ya shiga tare da yin tasiri sosai a zukatan miliyoyin ‘yan Jihar Neja da sauran ‘yan Nijeriya masu cike da sanin cewa babban burin Malagi shi ne ya bunƙasa Jihar Neja.

Watanni uku bayan zaɓen fidda gwani, yanzu shi ne ya kasance abin kwatance a faɗin jihar. Kowa ya na nuna so da shauƙin yin kusanci da shi. Ana yi masa kallon sani sabon tauraron siyasar Jihar Neja, wanda duk sauran jam’iyyu ke ta shauƙin neman ya canja sheƙa, ya koma cikin su, su tsayar da shi takarar gwamna kawai.

Mohammed Idris mai shekaru 56 a duniya, mawallafin jarida ne kuma ƙwarraren massnin iya hulɗa da jama’a, yanzu ya zama wata rana ce da ta fito a siyasar Jihar Neja, wadda tafin hannu ba zai iya rufe ta ba. Ko ma dai me za a sake nanatawa dangane da sakamakon zaɓen fidda gwani da yadda aka gudanar da zaɓen, za a iya cewa an ɗauki ƙwaƙƙwaran darasi don gaba.

Jibrin Ndace ɗan jarida ne mazaunin Abuja.

Tags: AbujaHausaLabaraiMohammedNajeriyaNejaNewsNigerPREMIUM TIMES
Previous Post

MURNA TA KOMA CIKI: Kotu a Jalingo ta kori Bwala daga takarar gwamna na jam’iyyar APC

Next Post

Yadda gogarman Dogo Giɗe ya auri Ƴa ta auren-dole – Sani Yauri, mahaifin Farida,’amaryar’ Dogo Giɗe

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Yadda gogarman Dogo Giɗe ya auri Ƴa ta auren-dole – Sani Yauri, mahaifin Farida,’amaryar’ Dogo Giɗe

Yadda gogarman Dogo Giɗe ya auri Ƴa ta auren-dole - Sani Yauri, mahaifin Farida,'amaryar' Dogo Giɗe

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru
  • TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa
  • FCT ABUJA: Wike ya kori shugabanni da daraktocin hukumomi 21
  • Kotu ta yi watsi da ƙarar PDP a Shari’ar gwamnan Kaduna, dalili kuwa shine wai ba ta shigar da ƙara da wuri ba
  • MASHAHURAN JAMI’O’IN DUNIYA: Jami’ar Bayero ta fita kunya, Covenant da UI ne kawai ke gaba da ita a Najeriya

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.