Lauya mai kare haƙƙin jama’a Femi Falana, ya maka Shugaba Muhammadu Buhari da Majalisar Najeriya a Babbar Kotun Tarayya, inda ya nemi kotu ta tilasta masu gaggauta samar da na’urorin inganta tsaro a dukkan gidajen kurkukun Najeriya.
Ya maka su ƙara watanni biyu bayan ‘yan ta’addar ISWAP sun ragargaza kurkukun Kuje, inda su ka fitar da kwamandojin su 64, kuma wasu ɗaurarru 800 su ka arce.
Falana ya haɗa har da Shugaban Gidajen Kurkukun Najeriya ya maka kotu, ya na so kotu ta jaddada masu cewa haƙƙin su ne su kare rayuka da lafiyar waɗanda ke tsare a gidajen kurkuku.
Ya nemi a samar da hasumiyar hangen mugaye daga nesa, doguwar katanga mai ƙarfin Mahadi-ka-ture, kyamarar ɗaukar hotunan bidiyon masu gilmawa a kusa da nesa, na’urar binciken jikin masu shiga da fita cikin kirkuku da sauran na’urorin gaggawa.
Falana ya buga misali da Sashe na 28 (1) na Dokar Gidajen Kurkuku ta Ƙasa, wadda ta nuna cewa gwamnati ce ke da haƙƙin kare su, ba waɗanda ke tsare ne ke da haƙƙin kare kan su ba.
Lauya Ayodele Aribisala na Ofishin Chambar Falana ne ya shigar da ƙarar a madadin mai ƙarar.
An shigar da ƙarar a ranar 23 Ga Agusta, inda ya roƙi kotu ta tilasta wa waɗanda ya ke ƙara su bi abin da doka ta tanadar wajen kare rayuka da lafiyar waɗanda ke tsare a kurkuku.
PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin cewa Minista Rauf Aregbesola ya ce akwai jami’an tsaro 65 lokacin da ‘yan ta’adda su ka mamaye wurin.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola ya ce akwai jami’an tsaro 65 masu ɗauke da makamai, a lokacin da ‘yan ta’adda su ka kai wa Kurkukun Abuja da ke Kuje hari watannin baya.
Aregbesola ya yi wannan bayani ranar Litinin a gaban Kwamitin Haɗin-guiwar Majalisar Tarayya.
Ya ce jami’an da ke wurin su 65 sun ƙunshi sojoji, NSCDC, na Hukumar Cikin Gida da sauran jami’an wasu ɓangarorin tsaro.
An dai kai harin a ranar 5 Ga Yuli, inda sama da ɗaurarru 800 su ka tsere, cikin su kuwa har da ‘yan Boko Haram wajen 64.
ISWAP, ɓangaren Boko Haram da su ka ɓalle daga ɓangaren Shekau sun ce su ne su ka ɗauki nauyin kai harin, wanda washegari har bidiyon yadda fasa bango da ƙofar gidan kurkukun sai da su ka watsa.
An riƙa mamakin yadda su kayi nasarar kai harin duk kuwa da cewa akwai dandazon sojoji a yankin Gundumar FCT.
Cikin watan Yuli Aregbesola ya ce ‘yan ta’addar sun ci ƙarfin “dukkan sojojin da ke wurin ne a lokacin da su ka kai harin.”
Sai dai kuma da Minista Aregbesola ke amsa tambayoyi a gaban Kwamitin Haɗin-guiwar Majalisar Tarayya, ya ƙi ya bayyana irin makaman da jami’an tsaron ke ɗauke da su, a lokacin da ISWAP su ka tarwatsa su, har su ka yi galabar shiga cikin kurkukun.
Aregbesola ya ce ba zai bayyana irin makaman da jami’an tsaron ke ɗauke da su ba, saboda akwai ‘yan jarida a cikin ɗakin binciken.
“A ranar da aka kai harin akwai sojoji 31, MOPOL 10, Jami’an Daƙile Ta’addanci 2, ‘Yan Sanda 2, Jami’an Tsaron Kurkuku 7, na NSCDC 3, sai na Gidan Kurkuku 10.
“Dukkan su an kai su ne domin su hana kai farmaki a gidan kurkukun, kuma kowanen su akwai makami a hannun sa.” Inji Minista Aregbesola.
Wani mamba ɗin kwamitin ne mai suna Ifeanyi Momah ɗan jam’iyyar APGA daga Anambra ya gabatar da roƙon a yi zaman kwamitin a bayyane. Hakan ta sa an ƙi amincewa da buƙatar Shugaban Kwamitin Sha’aban Sharaɗa, wanda ya nemi a yi zaman a cikin sirri.
Sha’aban ya yi ƙoƙarin a fitar da ‘yan jarida a wurin zaman sauraren, amma sauran mambobin kwamitin su ka ƙi amincewa.
Sai dai kuma a lokacin da ake yi wa Minista Aregbesola tambayoyi, ya ƙi bayyana wasu muhimman batutuwan da ya ba zai faɗa a gaban ‘yan jaridu ba, sai dai a asirce.
An Bai Wa Shugabannin Tsaro Gargaɗin Ƙarshe:
Kwamitin ya bai wa dukkanin shugabannin ɓangarorin tsaro gargaɗin cewa kowa ya bayyana a gaban kwamiti, ko a ɗauki tsatstsauran mataki a kan sa.
Mamba na kwamitin mai suna Nicolas Ossai (PDP, Delta), ya gabatar da roƙon a bai wa shugabannin tsaron gargaɗin ƙarshe su bayyana, kuma a aika wa duk wanda aka san ya ƙi zuwa wasiƙar gayyata ta ƙarshe. An kuma amince da yin haka ɗin.
Discussion about this post