Angola ta shige gaban Najeriya a matsayin ƙasar da ta fi sauran ƙasashen Afrika haƙo ɗanyen mai a kullum, inda a yanzu Angola na haƙo ganga miliyan 1.17 a kullum, Najeriya kuma ganga miliyan 1.13 a kullum.
Tsawon Shekaru 10 Najeriya ta shafe na ta matsayin ta farko wajen haƙo ɗanyen mai mai yawa a kullum, amma a cikin 2017 Angola ɗin dai ta taɓa shiga gaban Najeriya.
Satar Ɗanyen Mai: Haɗin Baki Tsakanin Ɓarayin Cikin Ofis Da Ɓarayin Cikin Daji:
Satar ɗanyen mai a yankin Neja Delta ta zama wata gagarimar hanyar satar dukiyar gwamnati, kuma hanyar da wasu ke samun mahaukatan kuɗaɗe.
Masu satar ɗanyen man su na da alaƙa da ‘yan siyasa, manyan jami’an gwamnati kai har ma a cikin sojoji.
Haka kuma yayin da wannan gagarimar satar ɗanyen mai da ake yi a yankin Neja Delta, ya na da barazanar lalata muhallin yankin.
Rigingimun yankin sun haifar wa Najeriya asarar dala biliyan 1 daga Janairu zuwa Maris, wato watanni uku kenan. Kuma ɓarayin ɗanyen mai ne ke ci gaba da satar kuɗaɗen.
Dala biliyan 1 kuma ta yi daidai da adadin kuɗaɗen da ake buƙata wajen samar wa mutum miliyan 4.1 abinci mai gina jiki a yankin Arewa maso Gabas ɗin ƙasar nan, kamar yadda Majisar Dinkin Duniya (UN) ta yi hasashe.
Idan aka ci gaba da haka a Najeriya, to Libiya ma wadda a halin da ake ciki yanzu ta na iya haƙo ganga miliyan 1.08, alamomi na nuna cewa idan Najeriya ta ci gaba a haka, to Libiya za ta doke ta.
Cikin Agusta Najeriya ta haƙo ganga 972, 200.
Wannan yawan satar ɗanyen mai kuwa ta janyo Najeriya ba ta amfana da tsadar da fetur ya yi a lokacin yanzu na yaƙin Rasha da Ukraniya.
Sauran dalilan sun haɗa da yawan kuɗin tallafin fetur da Najeriya ke yi.
Najeriya dai ta ce ta na sa ran kashe Naira tiriliyan 6.7 wajen biyan tallafin fetur a 2023.
Discussion about this post