Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai cilla kasar Amurka domin halartar taron majalisar ɗinkin duniya.
A sanarwar da Femi Adesina ya fitar kuma ya saka wa hannu ranar Asabar, shugaba Buhari zai tashi zuwa kasar Amurka ranar Lahadi, kuma zai yi jawabi a wurin taron majalisar ɗinkin duniya, a zauren UN din.
Haka shima mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya tashi zuwa kasar Birtaniya domin halartar Jana’izar marigayiya sarauniyar Ingila, Elizabeth wanda ta rasu a cikin makon jiya.
Mai taimaka wa Osinbajo kan harkokin yaɗa labarai Laolu Akande da shine ya fodda sanarwar ba faɗi ranar da mataimakin shugaban kasan zai dawo Najeriya ba.
Discussion about this post