‘Yan bindiga da ake zargi Fulani ne sun yi garkuwa da mutane a hanyar Enugu zuwa Fatakwal dake tsakanin kauyukan Leru da Ihube dake jihohin Abia da Imo ranar Asabar.
Maharan wanda suka tsare hanyar sun fi 30 sannna sun yi awon gaba da duk fasinjojin dake motoci uku.
‘Yan bindigan sun Kuma bude wa motan sojoji wuta wacce ta zo kawo dauki inda sojoji biyu suka ji rauni.
Wani shugaban matasa na kauyen da baya so a fadi sunan sa ya ce harin ya tsorata mutane da dama a kauyen samman matafiya da suka biyo hanyar sun dauka jami’an tsaro ne yayin da suka hango maharan.
“Sai dai wasu sun ji raunin harsashi a jikinsu a lokacin da maharan suka bude wa motan sojoji wuta a wurin.
Kwamishinan yada labarai kuma sakataren dakile matsalar rashin tsaro na jihar Abia Chikamnayo Eze ya ce harin ya faru a bangaren jihar Imo ne.
Eze ya ce jihar Abia ta samu nasarar rage yawan hare-haren da ‘yan bindiga ke kai wa mutane a jihar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Geoffery Ogbonna bai amsa wayar salulansa ba da sakonin tes din da aka aika wa wayarsa ba game da harin.
Ci gaba da garkuwa da mutane a jihar Abia.
Yin garkuwa da mutane domin karban kudaden fansa ya zama ruwan dare a jihar Abia.
Garkuwa da mutanen da aka yi ranar Asabar din da ya gabata ya faru bayan sati daya da ‘yan bindiga suka yi awon gaba da wasu matafiya a kauyen Lokpanta dake karamar hukumar Umunneochi jihar Abia.
A tsakiyar watan Yuni ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ma’aikacin gidan jarida a Umuahia.
Maharan sun sako ma’aikacin bayan da aka biya naira miliyan 10 kudin fansan sa.
A farko watan Yuni ‘yan bindiga sun sace likita kuma shugaban fannin koyar da likitanci dake Jami’ar Gregory dake Umuahia Uwadinachi Iweha.
Maharan sun sace Iweha a lokacin da yake fitowa daga cikin gidansa dake Umuajameze Ezeleke Umuopara a karamar hukumar Umuahia ta Kudu.
Likitan ya yi tsawon watanni biyu kenan a hannun maharan sannan har yanzu ba su sake shi ba.
Daga nan kuma a watan Mayu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da babban limamin cocin Methodist ta Najeriya Samuel Kanu-Uche tare da wasu fastoci biyu a hanyar su ta zuwa karamar hukumar Umunneochi.
‘Yan bindiga sun saki fastocin bayan an biya naira miliyan 100.
Discussion about this post