‘Yan bindiga sun kai hari kwatas din Shola dake cikin garin Katsina inda suka kashe wasu ‘yan banga biyu, sannan suka yi garkuwa da mazauna wannan rkunin gidaje da dama.
Daga cikin mutanen da maharan suka yi awon gaba da su akwai sabon ango da amaryarsa.
Kwatas din Shola na tsakiyar cikin garin Katsina ne kuma yana bayan babban asibitin koyarwa na Umaru Musa Yar’adu’a.
Akwai manyan shagunan da gidajen manyan ma’aikatan gwamnati a wannan wuri.
Mazauna kwatas din sun bayyana wa PREMIUM TIMES cewa maharan sun dauki sama da awa daya suna cin karen su ba babbaka tare da jami’an tsaro sun zo kawo dauki ba, sai dai yan banga da suka fafata da su.
“Sai da garin Allah ya waye sannan muka garzaya da ‘yan bangan da suka ji rauni asibiti sannan muka yi jana’izar wadanda suka mutu.
Wani dan uwan ango da amaryar da maharan suka yi garkuwa da su Usman Masanawa ya ce maharan basu shiga gidan dan uwansa ta kofar shiga ba, fasa bangon gidan suka yi suka kutsa suka dauko shi da amaryar sa.
“Na yi zaman wannan kwatas din amma da na ga kai wa wurin hari ya yi yawa sai na tattara na canja wurin zama.
” ko da yake ko a alokacin da maharan ke kokarin arcewa da Bashir ya kira ta waya amma tsakani da Allah babu abinda zan iya yi sai dai kawai na yi ta addua har aka waske da shi da sabuwar Amaryar sa.
Sannan da muka zo gidan da safe mun iske yadda maharan suka fasa bangon gidan suka shiga suka yi awon gaba da su.
“Har yanzu ba mu da masaniyar yawan mutanen da aka yi garkuwa da su ba.
Masanawa ya ce baya ga ‘yan sa kai biyu din da suka ji rauni wasu mazaunan kwatas din sun ji rauni daga harbin bindiga yanzu haka suna asibiti.
Discussion about this post