• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

YAƘIN 2023: Yadda Babachir Lawal da Yakubu Dogara ke wa Tinubu yaƙin-sunƙuru saboda takarar ‘Muslim-Muslim’

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 1, 2022
in Labarai
0
YAƘIN 2023: Yadda Babachir Lawal da Yakubu Dogara ke wa Tinubu yaƙin-sunƙuru saboda takarar ‘Muslim-Muslim’

Saɓani, rashin jituwa da rikici a kan takarar Muslim-Muslim ta Bola Tinubu da Kashin Shettima a APC, ta ƙara muni da tayar da ruɗani a cikin APC a makon jiya, yayin da wasu manyan jam’iyyar su ka tabbatar cewa sai sun kunyata APC a zaɓen 2023.

Lamarin ya yi tsamarin da tsohon Kakakin Majalisar Tarayya Yakubu Dogara da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal su ka kira taron Manyan Kiristocin Arewa ‘Yan APC, a ranar Juma’a a Abuja, su ka yi wannan barazana.

Dama kuma Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta yi tofin tsinuwa kan ɗaukar Shettima a matsayin mataimakin takarar shugaban ƙasa na APC, inda ƙungiyar ta ce cin mutunci ne ga ɗaukacin kiristocin Najeriya.

Yi wa lamarin tir ya ƙara ƙamari lokacin da aka yi zargin APC ta ɗauki sojojin hayar fasto-fasto na bogi, su ka shiga taron ƙaddamar da Shettima. A nan ma CAN ta yi tir da lamarin.

Tawayen Dogara Da Babachir Lawal:

Kafin Lawal da Dogara su haɗa ƙarfi wuri ɗaya, Babachir Lawal tuni ya fito ya nemi Shugaba Muhammadu Buhari ya ƙi amincewa da Shettima, domin a cewar sa, an yi wa Kiristocin Arewa rashin adalci. Sai dai kuma Buhari bai yi hakan ba.

Babachir na daga cikin ‘yan kwamitin da su ka bayar da shawarar wanda Tinubu ya kamata ya ɗauka.

Jin haushin ɗaukar Shettima ya sa Babachir ya ƙudiri aniyar tarwatsa ƙudirin APC. “Tuni an ba mu goron gayyata zuwa yaƙi. Har mun isa sansani, mun kafa tantina.” Inji Babachir.

Za Mu Yi Amfani Da Katin Zaɓe Mu Murƙushe Takarar ‘Muslim-Muslim’ A 2023:

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya Babachir Lawal da tsohon Kakakin Majalisar Tarayya, Yakubu dogara, sun ƙara fitowa fili sun nuna rashin amincewar kan takarar Bala Tinubu da Kashin Shettima a APC, takarar da ake kira ‘Muslim-Muslim Ticket’, saboda su biyun duk Musulmai ne.

Babachir Lawal ya ce Kiristoci ‘yan APC za su yi amfani da katin zaɓen su domin su koya wa APC hankali, tunda hankalin ta ya gushe a jikin ta.

Babachir ya ce duk zancen banza ne da ake cewa wai cancanta ce ta sa Tinubu ya ɗauki Kashim Shettima ya yi masa takarar mataimaki, ba addini ba.

Lawal ya ce tsarin ‘Muslim-Muslim’ wata daɗaɗɗiyar ajanda ce ta ture Kiristoci daga mulkin ƙasar nan.

Ya buga misali da ɗaukar Kashim Shettima matsayin mataimakin takarar Tinubu, rashin Kiristoci Kwamitocin NWC da NEC na jam’iyyar APC, ya ce duk tuggun ture Kiristoci ne.

“Kada ma a kawo mana wani rainin wayau a ce wai babu ruwan addini idan ana maganar siyasa. Domin abin da ke faruwa a APC daɗaɗɗen shiri ne sai yanzu aka samu damar fito da shi.

Saboda haka ya ce tun da wuri bai kamata APC ta ci gaba da tafiyar ‘Muslim-Muslim Ticket’ ba, saboda ba wani abin alherin da zai kawo, sai dai ƙara rarrabuwar kawuna tsakanin Musulmi da Kirista a Najeriya.

Shi ma tsohon Kakakin Majalisar Tarayya Yakubu Dogara, ya yi fatali, tir da Allah–wadai da abin da APC ta yi, wanda ya ce babban kuskure ne da rainin wato, a ce duk cikin Kiristocin Arewa babu wanda zai iya zama ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a APC.

“Tinubu ya yi babban kuskure tunda har ya biye wa gungun waɗanda su ka kitsa tuggun raina mana wayau.”

Dogara ya ce Kiristocin APC za su yi amfani da katin zaɓe domin su koya wa APC hankali.

Cikin manyan baƙi har da Sanata Elisha Agbo da Solomon Dalung.

“Wannan rainin hankali da aka yi mana, zai zama tayar da mu ne daga barci aka yi wa mu Kiristocin Najeriya. Ba mu muka fara wannan siyasar addini ba. APC ce da ‘yan takarar ta su ka fara. Don haka kowanen mu ya tashi tsaye ya yi abin da ya dace mu yi.”

Kun Shigo Da Siyasar Nuna Fifiko Da Raba Kawuna A APC -Dogara:

Dogara ya ce takarar ‘Muslim-Muslim’ siyasar nuna fifiko ce aka yi wa Kiristocin Najeriya, kuma an dasa bambanci da rabuwar kawuna kenan.

Bayan taron manyan Kiristoci a Abuja, Dogara da Babachir sun ziyarci Gwamna Samuel Ortom na Benuwai da Nysome Wike na Ribas.

Ya Tasiri Yaƙin Tawayen Da Dogara Da Babachir A APC?:

Duk da dai Shugaban APC Abdullahi Adamu da Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje sun ragargaji Babachir da masu sukar Tinubu saboda ya ɗauki Shettima takarar mataimakin sa.

Ganawar Manyan ‘Yan Tawayen APC Da Wike:

Shi ma Wike da ya karɓi baƙuncin Dogara da Babachir, ya na da jiƙaƙƙa mai tsamari tsakanin sa da Atiku Abubakar, ɗan takarar PDP na zaɓen 2023. Matsalar ta su ta bijiro ne kan fitar da ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na PDP, inda ta kai har kwana ɗaya kafin ziyarar Dogara da Babachir, sai da Wike ya buɗe wa Atiku wuta, tare da kiran sa tantagaryar maƙaryaci, a wani raddi da ya mayar wa Atiku ɗin.

Saboda haka idan ma Dogara da Babachir na son kamun-ƙafar haɗa kai da PDP ne, to Wike ba zai kasance ɗan jagoran da zai kai su ga nasara ba

Kwanan baya shi ma Wike ɗin an ce ya karɓi baƙuncin gwamnoni uku na jihohin Yarabawa masu kusanci da Tinubu. Wasu na ganin cewa Tinubu ne ya turo su wajen Wike ɗin. Shin ko kuwa Dogara da Babachir sun gargaɗi Wike kada ya haɗa kai da APC ne?

Su ma su Dogara da Babachir har yau ba mu ji sun gana da Gwamnonin APC ba. Shin ko gwamnonin babu ruwan su da sha’anin na su ne, su biyu ke kiɗan su, kuma su ke yin rawar su ne?

APC na da Gwamnoni Kirista 6 cikin 22 da ta ke da su a ƙasar nan. Simon Lalong na Filato ne kaɗai Gwamna Kirista a APC a Arewa, kuma sunan sa na cikin sunayen da aka bai wa Tinubu domin ya zaɓi ɗan takarar mataimaki a cikin su. An ce an haɗa da sunayen Babachir da na Dogara. Amma sai Tinubu ya ɗauki sunan Shettima, Musulmi kamar sa. Wannan abu ya ɓata wa Kiristoci rai, musumman ma na Arewa.

Har yau ba a ji Lalong ya caccaki ɗaukar Shettima ɗan takarar mataimaki ba. Sai ma ji aka yi shi ne za a naɗa daraktan kamfen ɗin TInubu.

Sauran Gwamnonin APC biyar duk a kudancin Najeriya su ke. Dukkan su kuma su na yin kalamai ne cikin taka-tsantsan, su na cewa a daina gwamutsa siyasa da addini.

Tsinkayen Da Sule Lamiɗo Ya Yi Wa Rikicin APC:

“Idan da a cikin 2007 ne aka haka, ba komai. Amma yanzu ana yaɗa farfagandar addini a cikin siyasa, har ta rigaya ta yi tasiri. Malamai na magana kan siyasa. Kiristoci na magana kan siyasa. Ba suran mai magana da muryar Najeriya.

“Duk abin da Tinubu zai samu a Arewa, ba zai same shi a Kudu ba. Ni dai ban ga wannan lamari zai iya kai Tinubu gaci ba.”

Tags: AbujaBabachirHausaNewsPREMIUM TIMESYakubu Dogara
Previous Post

2023: INEC za ta raba katin zaɓe cikin Oktoba da Nuwanba – Okoye

Next Post

KWANA ƊAYA BAYAN GANAWAR WIKE DA SU DOGARA: Wike ya karɓi baƙuncin Gwamnonin PDP na yanzu da na da can

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
KWANA ƊAYA BAYAN GANAWAR WIKE DA SU DOGARA: Wike ya karɓi baƙuncin Gwamnonin PDP na yanzu da na da can

KWANA ƊAYA BAYAN GANAWAR WIKE DA SU DOGARA: Wike ya karɓi baƙuncin Gwamnonin PDP na yanzu da na da can

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai
  • HAJJI 2023: Hukumar Alhazai ta gindiya sabbin sharuɗɗan adadin kwanakin ziyara Madina
  • HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125
  • KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu
  • DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.