Shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Zailani ya karyata raderadin da ake ta yadawa wai majalisar jihar Kaduna karklashin shugabancin sa za ta tsige gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai.
An buga a wasu shafukan ƴaɗa labarai wai majalisar Kaduna ta gano wasu harkallar makudan kudade da aka yi sama da fadi da su a wasu ma’aikatun gwamnatin jihar Kaduna wanda da sanin gwamna El-Rufai aka handame su. Dalilin haka ya sa wai majalisar karkashin shugaban ta Yusuf Zailani ta fadada bincike akai kuma ta gano cewa lallai an aikata hakan kuma dalilin haka ya sa majalisar zata gudanar da bincike da tsige gwamnan jihar.
Rahoton ya ce majalisar ta gama shiri tsaf da zarar ta kammala bincike zata tsige gwamnan.
Sai dai kuma Sipika Zailani ya karyata hakan a wata sanarwa da ofishinsa ta fitar ranar Lahadi, yana mai cewa makiyan jihar Kaduna ne suka kitsa wannan makirci domin raba kan majalisar da kuma tarwatsa zaman lafiya dake tsakanin majalisar da gwamna El-Rufai.
” Babu magana mai kama da irin haka ma. Wasu ne kawai da basu son suga ana zaman lafiya suka kitsa haka. Amma tsakanin majalisar jihar Kaduna da bangaren zartaswa, suna zaman lafiya babu wani abu da ya shiga tsakanin su.
” Saboda haka ina kira ga mutanen jihar Kaduna da su yi watsi da wannan labari su cigaba da al’amuran su. ko mai yana nan lafiya cikin lafiya da aminci da kauna a tsanin gwamna El-Rufai da majalisar jihar.
Discussion about this post