• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TARANGAHUMAR TALLAFIN FETUR: Kamfanin A-Z ya roƙi Majalisar Tarayya ta ƙwato masa haƙƙin naira biliyan 30 daga hannun Gwamnatin Tarayya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 11, 2022
in Rahotanni
0
KISAN GILLAR ZABARMARI: Majalisar Tarayya ta aika wa Buhari Sammaci, ya gaggauta bayyana a gabanta

Wani kamfanin mai da ake kira A-Z Petroleum Ltd., ya roƙi Majalisar Tarayya ta sa baki domin gwamnatin tarayya ta biya shi bashin naira bilyan 30 da ya ce kuɗaɗen tallafi ne waɗanda Gwamantin Tarayya ta ƙi biyan sa.

Wannan bayanin na ƙunshe cikin jawabin da wakilin kamfanin mai suna Hafford Udochukwu ya yi wa Kwamitin Binciken Adadin Fetur ɗin da ake sha kullum a Najeriya.

Ya ce a cikin 2015 A-Z ya shigo da fetur lita miliyan 245.89. Cikin 2017 ya shigo da lita miliyan 26.27, sai kuma cikin 2018 ya shigo da fetur lita miliyan 26.64.

Ya ce rabon da Gwamnatin Tarayya ta biya shi kuɗaɗen tallafi tun cikin 2017. Dalilin haka a cewar sa, yanzu kamfanin ya durƙushe ya daina hada-hadar kasuwanci, saboda gwamnatin tarayya ta riƙe masa haƙƙin sa, alhali tuni duk ta biya sauran kamfanoni.

Ya ce bashin da A-Z ke bin gwamnati ya kai na naira bilyan 30.

Shugaban Kwamitin Bincike Abdulƙadir Abdullahi daga Jihar Kano ya buƙaci Udochukwu ya gabatar da kwafen takardun shaidar kuɗaɗen da ya ke bin gwamnatin tarayya bashi.

A dai ranar Laraba ɗin ce Majalisar Tarayya ta umarci Ministar Kuɗaɗe ta bada takardar bayanan biyan kuɗaɗen tallafin fetur daga 2013 zuwa 2022.

Majalisar Tarayya ta umarci Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed ta gaggauta bayyana domin gabatar da adadin kuɗaɗen da aka biya dalla-dalla, da sunan biyan talalfin fetur.

Shugaban Kwamitin Binciken Kuɗaɗen Fetur, Aliyu Musa ne ya bayar da wannan umarni a ranar Talata, lokacin da Daraktan Harkokin Kuɗaɗe na Cikin Gida a Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ya bayyana a gaban kwamitin.

Kwamitin dai tun da farko ya bayar da wa’adin zuwa ranar 16 Ga Agusta domin a kai masa kwafen bayanan da su ka haɗa da:

Jimla da dalla-dallar adadin kuɗaɗen da aka gabza daga cikin Asusun Haɗaka na tara kuɗaɗen haraji aka biya tallafin fetur da su, tun daga 2013 zuwa yau 2022 da ake ciki.

Kwamiti ya kuma nemi a kai masa dukkan kwafe-kwafen takardun biyan kuɗaɗen da aka ce an yi.

Kwamitin bincike ya kuma nemi a kai masa sunayen dukkan kamfanonin da aka taɓa biya kuɗaɗen tallafin fetur da adadin da aka riƙa biyan kowane.

Wannan tashin-balli ya zo ne bayan Minista Zainab ta bayyana cewa Najeriya na buƙatar naira tiriliyan 6.7 domin ta biya tallafin fetur da kuɗaɗen.

Aliyu ya ce wannan lamari abin damuwa ne matuƙa.

“Dole Minista ta bayyana domin gabatar da bayanai masu damun ‘yan Najeriya. Ciki har da shirin da gwamnati ke yi domin ciwo bashi a biya tallafin fetur da kuɗaɗen bashin.

Wanan binkice na faruwa ne makonni biyu bayan Minista Zainab ta ce tattalin arzikin Najeriya ya kusa durƙushewa; an gano saura dala biliyan 15 a asusun waje, ba dala biliyan 36 da CBN ya ce saura ba.

Yayin da Najeriya ke shirin zaɓen 2023 cikin shekara mai zuwa, hujjoji na ƙara bayyana cewa tattalin arzikin ƙasar fuskantar matsanancin yanayi biyu: wato baitilmalin da ba ko ranyo a ciki, sai kuma raguwar da tattalin ke yi a kullum.

Jami’an gwamnati da manyan ‘yan kasuwar da ke da masaniyar halin da ake ciki, sun ce ana nuna damuwa sosai a Abuja da Legas, yayin da wani zaɓaɓɓen jami’in gwamnati ya jawo hankalin Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele cewa abin da ya rage a asusun Najeriya da ke waje fa bai wuce dala biliyan 15 ba, wato ƙasa sosai da dala biliyan 36 ɗin CBN ɗin ya yi iƙirarin cewa su na cikin asusun.

Yayin da Najeriya ta kashe naira tiriliyan 5.9 wajen shigo da kayayyaki daga waje tsakanin Janairu zuwa Afrilu 2022 kaɗai, dala biliyan 15 kacal ɗin ƙasar ke da shi a yanzu ba su wuce kashewa cikin watanni huɗu kacal ba kenan wajen shigo da kayayyaki.

Masana harkokin tasarifin kuɗaɗen sun ce da a ce komai na tafiya daidai, to raguwar kuɗaɗen ba abin damuwa ba ne. Amma abin fargabar shi ne yadda aka shafe watanni shida cur Najeriya ba ta zuba ko sisi a cikin asusun don kuɗin su ƙaru ba. Wannan kuma ya faru ne saboda matsalar rashin wadatar ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa waje ne, da kuma tsayuwar gwanin jakin da kasuwar ta yi.

Sannan kuma ɗaukar lokaci mai tsawo da NNPC ta yi ta kada zuba cinikin ɗanyen mai a CBN, shi ne ya haifar da tsawwala farashin dala a kasuwannin ‘yan canji.

Wata babbar ma’aikaciyar banki wadda ta ce wannan jarida ta rufa mata asiri kada ta ambaci sunan ta, ta ce an daɗe ana ɓoye gaskiyar sauran adadin kuɗaɗen gwamnati a cikin asusun waje, wanda babbar matsala ce sosai a halin yanzu.

Ta ce an yi ƙarin gishiri ne wajen ainihin yawan kuɗaɗen da ke CBN, domin kawai a ɓoye ainihin adadin da su ka rage a asusun waje.

An haƙƙaƙe cewa wannan babban jami’in gwamnati wanda kuma zaɓen sa aka yi, ya sanar wa Shugaba Muhammadu Buhari gaskiyar halin da ake ciki na ramewar tattalin arzikin Najeriya. Sai dai kuma Fadar Shugaban Ƙasa ba ta amsa wa PREMIUM TIMES tambayoyin da ta yi kan wannan mawuyacin halin da ake ciki ba.

Sannan kuma maida NNPC hannun jarin masu kasuwanci da aka ce an yi, ya ƙara dagula matsalolin. Wato tunda NNPC ya kasa zuba kuɗaɗen cinikin ɗanyen mai ko na fetur a asusun CBN, tilas kenan bankin ya tashi ya inda zai samu manyan kuɗaɗen ƙasashen waje.

Abin damuwa a nan shi ne, mafi yawan hanyoyin da CBN zai iya samun kuɗaɗen duk a toshe su ke da majinar murar da ta toshe hancin CBN ɗin, wanda kuma shi da kan sa ya ƙirƙiri tsarin da ya haifar da toshewar ƙofofin hancin na sa.

Ma’ana dai tunda asusun ajiyar kuɗaɗe na waje an kasa saka masa komai tsawon watanni huɗu, to ƙasar nan ba ta da sukunin iya biyan kuɗaɗen abinci, magunguna da kayan ayyuka daban-daban da ake buƙatar shigo da su a masana’antun mu. Wato dai irin matsalar tattalin arzikin da Sri Lanka ke fuskanta a yanzu kenan.

Maganar dai kai tsaye ita ce Najeriya na fuskantar mummunar matsalar ƙarancin kuɗi, ga wawakeken giɓin kasafin kuɗi, tulin basussuka da kuma taguwar da kuɗaɗen shigar da ƙasar ke samu ke yi a kullum.

Cikin Yuli PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda matsalar ƙarancin kuɗaɗe ta yi wa Najeriya rumfa inda a cikin watannin Janairu zuwa Afrilu kuɗaɗen da ƙasar ta biya bashi, sun haura kuɗaɗen shigar da ta samu a cikin waɗancan watannin huɗu.

Kafin NNPC ta kasa ci gaba da zuba kuɗin cinikin ɗanyen mai a CBN, a duk wata ta kan zuba dala biliyan 3 daga ɗanyen man da Najeriya ta sayar a watan. Amma kuma kusan shekara ɗaya kenan NNPC ba ta zuba abin da ya kai ko da dala miliyan 200 ba.

Cikin watan jiya ne Ministan Ƙwadago Chris Ngige ya ce a kwantar da hankali tare da yin taka-tsantsan, saboda fatara da talauci sun yi wa Najeriya tarnaƙi da dabaibayi. Ta kai babu kuɗaɗen da ƙasar za ta biya manyan ayyukan raya ƙasa a shekara mai zuwa. Hakan na nufin lamarin zai ƙara munana matsalar rashin aikin yin da ake fama da ita, sai kuma ƙaruwar malejin ƙuncin rayuwa da hakan zai haifar kenan a shekara mai zuwa.

Cikin makon juya ne kuma Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed ta ce Gwamnatin Tarayya ta kamfaci dala biliyan 1 daga Asusun Rarar Kuɗin Fetur, domin inganta tsaro.

Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta kwashi naira biliyan 1 daga Asusun Rarar Kuɗin Fetur (ECA), domin inganta harkokin tsaro, a daidai lokacin da kuɗaɗen shiga daga fetur ke ƙara raguwa sosai.

Zainab ta yi wannan bayani a gaban manema labarai, ranar Laraba, a fadar Shugaban Ƙasa, ƙarshen zaman su da Shugaba Muhammadu Buhari.

Waɗannan kuɗaɗe da Zainab ta ce an kamfata, lamarin ya zo ne daidai lokacin da ake kukan cewa kuɗaɗen asusun sun ragu sosai da sosai.

Rahotanni sun ce kuɗaɗen da ke cikin asusun sun ragu daga dala miliyan 35.7 a cikin Yuni 2022 zuwa dala 376,65.09 a ranar 25 Ga Yuli, 2022.

Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito cewa Akanta Janar ne ya bayyana sauran adadin a ranar Talata, amma bai faɗi dalilin raguwar kuɗaɗen ba.

A ranar Laraba dai Minista Zainab ta ce wutsilniyar da kasuwar ɗanyen mai ke yi a duniya ce ta tankwafe asusun har kuɗaɗen su ka ragu.

“Tsawon shekaru huɗu kenan ba mu saka ko sisi a cikin Asusun Rarar Ribar Fetur ba, saboda faɗi-tashin da kasuwar ɗanyen mai ke yi a duniya.” Inji Zainab.

“To abin da mu ke da shi a cikin asusun ne mu ka riƙa cira a hankali ana yin wasu ayyuka da su. Kuma duk lokacin da za a yi amfani da kuɗaɗen, sai an nemi shawarar Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa, wato gwamnoni, saboda asusu ne na Gwamantin Tarayya.

“Kuɗin da aka cira daga asusun a baya-bayan nan, su ne dala biliyan 1 domin a inganta harkokin tsaro. Kuma duk abin da ake cira sai da sanin Gwamnoni.”

Tags: BuharifeturNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

KAƊA HANTAR PDP: Wike ya gayyaci Gbajabiamila da Gwamnan Legas buɗe ayyukan taya jiha, bai gayyaci ‘yan PDP ba

Next Post

Kotu ta soke gabagaɗin da Minista Malami ya yi na yi wa Hukunce-hukuncen Ƙa’idojin Ƙwararrun Lauyoyi kwaskwarima

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
WALLE-WALLE DA KUƊAƊEN SATA: Minista Malami ya ce bai yi wa Najeriya sagegeduwar ƙwato daloli biliyan 60 daga Amurka ba

Kotu ta soke gabagaɗin da Minista Malami ya yi na yi wa Hukunce-hukuncen Ƙa'idojin Ƙwararrun Lauyoyi kwaskwarima

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ba ni kaɗai ne na fidda sunan Ahmed Lawan ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu ba, akwai wasu da ke bayan fage – Adamu
  • Yadda bashin da Chana ta hana Najeriya ya kawo cikas a noman shinkafa, da aikin titin jirgin ƙasan Ibadan zuwa Kano
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: ‘Ban so Najeriya ta afka cikin raɗaɗin ƙuncin da ake fama da shi ba’ – Tinubu
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: ‘Za yi wa masu ƙaramin albashi ƙarin Naira 25,000 tsawon watanni 6 a jere
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: Fassarar Jawabin Shugaba Tinubu:

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.