Saboda jin raɗaɗin ƙalubalen matsalolin da su ka dabaibaye gwamnatin sa, Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana cewa har ya ƙagara ya bar ofis, bayan kammala wa’adin sa. Buhari ya yi wannan furuci ne lokacin da Gwamnonin APC su ka kai masa ziyarar gaisuwar Babbar Sallah a Daura.
Ɗaya daga cikin matsalolin da suka yi wa gwamnatin sa tarnaƙi da dabaibayi, ita ce matsalar cin hanci da rashawa, abin da ya yi kamfen a 2015 cewa idan ya hau mulki zai daƙile. “Idan ba mu kashe rashawa ba, to rashawa za ta kashe mu.” Haka ya riƙa faɗa a wancan lokacin.
Sai dai kuma abin baƙin ciki shi ne wannan annoba ya kasa kakkaɓe ta, sai ma cewa ake yi ta na ƙara ƙamari a gwamnatin sa.
Ƙarin abin takaici shi ne fifita makusanta da bangaranci wajen naɗa manyan muƙamai a gwamnatin Buhari, ya ƙara fifita wutar cin hanci da rashawa.
Yanzu haka Kwamitin Majalisar Tarayya na gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike kan harƙallar biyan kuɗin tallafin fetur, wanda ya rarake aljihun gwamnatin tarayya tsawon shekaru da dama.
Babban abin mamaki ne kuma abin takaici a ce tun daga Shugaban Ƙasa wanda shi ne Ministan Fetur, Ƙaramin Ministan Fetur da Ministar Harkokin Kuɗaɗe, dukkan su babu mai iya bayyana yawan adadin fetur ɗin da ake sayarwa kullum a Najeriya. Ballantana kuma a ce ga iyakar adadin kuɗaɗen tallafin da ake biya.
Kwamitin Majalisa ya yi ƙiyasin ana shan lita miliyan 40 zuwa miliyan 45 kullum a Najeriya. Amma kwamitin ya damu saboda NNPC Ltd na amfani da ƙididdigar cewa ana shan lita miliyan 65 zuwa miliyan 1000 a kullum, kuma ta hanyar amfani da waɗannan adadi ana cire masu kuɗaɗen tallafin fetur. Haka NNPC Ltd ya bayyana a cikin rahoton sa na wata-wata, wanda ta damƙa wa Kwamitin Rarraba Kuɗaɗen Tarayya.
Bambancin waɗannan adadi da ke tsakanin miliyan 40-45 da kuma miliyan 65 zuwa miliyan 100, ya nuna irin yadda ake tantagaryar wawurar kuɗaɗe a tsawon shekaru fiye da bakwai na mulkin Buhari.
Ƙarin abin takaici kuma shi ne jami’an tsaro da ke kula da kan iyakokin Najeriya ba su iya hana fasaƙwaurin fetur ana shiga da shi cikin ƙasashen da ke maƙwautaka da Najeriya.
Cikin wani ƙorafi da Honorabul Sergius Ogun ya gabatar, ya ce akwai ƙwararan hujjojin da ke nuni cewa ana ruɓanya kuɗaɗen tallafin da ake fitarwa kan fetur a NNPC Ltd, da kuɗaɗen tallafin da ake cirewa a ɗanyen mai NAPIMS, waɗanda adadin su zai iya kai naira tiriliyan 2.” Inji shi.
Amma abin haushi kawai ba tare da yin wani ƙwaƙƙwaran bincike ba, sai Shugaba Buhari ya a cikin Afrilu ya sa hannun amincewa da wani daftarin da aka kai masa na ƙara kuɗaɗen tallafi da naira tiriliyan 4.
Watau dai a ƙarshen bincike za a ɓallo wata badaƙala irin wadda aka taɓa ɓallowa cikin 2012.
Daga cikin naira tiriliyan 2.5 ɗin da a wancan lokacin aka ce an cire matsayin kuɗin tallafin fetur, an gano cewa an yi wa ‘yan damfara watandar naira tiriliyan 1.7, mutanen da ko galan ɗaya na man kaɗanya ba su taɓa shigo da shi Najeriya sun sayar ba, ballantana man fetur.
Waɗanda aka kama da laifi a lokacin sun haɗa da hukumomin gwamnati irin su NNPC. Tilas ta sa gwamnati ta rage tallafin mai a lokacin zuwa naira biliyan 971 tsakanin 2013 da 2014.
Honorabul Ogun ya ce a gefe ɗaya kuma ana ci gaba da taɓka satar ɗanyen mai, har ta kai Najeriya ba ta iya haƙo ganga miliyan 1.8 da OPEC ta amince ta riƙa haƙowa a kullum, ta ɓuge ta na haƙo ganga miliyan 1.25 a kullum kaɗai.
Tashar Bonny wadda tashar lodi a ruwa ce da ya kamata a ce ana loda ganga 200,000 a kullum, yanzu bai fi a loda ganga 3,000 kacal a kullum ba. Kuma har yau ba a kama kowa ba, ballantana a hukunta masu yin harƙallar.
A gefe kuma lamari ya yi lalacewar da Najeriya ta biya naira tiriliyan 1.9 matsayin kuɗaɗen bashi tsakanin Janairu zuwa Afrilu 2022. Adadin ya wuce kuɗaɗen da gwamnati ta tara naira tiriliyan 1.2 a watannin huɗu kenan.
Kuɗaɗen haraji ko kuɗaɗen shigar gwamnati na ci gaba da kauce hanya su na faɗawa aljifan asusun bankunan bogi na ma’aikatu dachukumomi da cibiyoyin gwamnati, tare da hadin baki da bankuna, waɗanda su ke kaucewa daga bin tsarin Asusun Bai Ɗaya (TSA) na Gwamantin Tarayya.
Ba mamaki da Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed ta ce sama da naira tiriliyan 5.2 na hannun Hukumomin Gwamnatin Tarayya, amma kuma naira biliyan 53.5 kaɗai aka samu damar karɓowa zuwa Afrilu, bayan an shafe watanni 18 ana gaganiyar ƙwatowa.
Ku dubi yadda tsohon Shugaban Kwastan ɗin da ya saci naira bilyan 40, ya maida naira biliyan 1.5 kacal, bayan amincewa da yin hakan da aka yi da shi. Lamarin da ya maida kamfen ɗin yaƙi da cin hanci na Gwamnatin Buhari wani wasan kwaikwayo.
Sannan kuma duk wani tsari da zai bari har Akanta Janar na Najeriya ya kantara satar naira biliyan 109, to ba tsarin kirki ba ne.
Sannan kuma duk wani ƙoƙarin da EFCC ke yi, to katsalandan ɗin da Ministan Harkokin Shari’a Abubakar Malami ya riƙa yi wajen yaƙi da masu wawurar kuɗaɗe, ya zubar da darajar ƙoƙarin da hukumar ke yi. Malami, wanda shi ne Antoni Janar na Ƙasa, wanda shi ne oga kwata-kwata na gabatar da manyan kuraye a kotu, kwanan nan ya auri ‘yar Shugaba Muhammadu Buhari.
Discussion about this post