• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Tarayya ta umarci Ministar Kuɗaɗe ta bada takardar bayanan biyan kuɗaɗen tallafin fetur daga 2013 zuwa 2022

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 10, 2022
in Manyan Labarai
0
Tulin bashin da Najeriya ke ciwowa ba mai kumbura ciki ba ne – In ji minista Zainab

Muhammadu Buhari and Zainab Ahmed

Majalisar Tarayya ta umarci Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed ta gaggauta bayyana domin gabatar da adadin kuɗaɗen da aka biya dalla-dalla, da sunan biyan talalfin fetur.

Shugaban Kwamitin Binciken Kuɗaɗen Fetur, Aliyu Musa ne ya bayar da wannan umarni a ranar Talata, lokacin da Daraktan Harkokin Kuɗaɗe na Cikin Gida a Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ya bayyana a gaban kwamitin.

Kwamitin dai tun da farko ya bayar da wa’adin zuwa ranar 16 Ga Agusta domin a kai masa kwafen bayanan da su ka haɗa da:

Jimla da dalla-dallar adadin kuɗaɗen da aka gabza daga cikin Asusun Haɗaka na tara kuɗaɗen haraji aka biya tallafin fetur da su, tun daga 2013 zuwa yau 2022 da ake ciki.

Kwamiti ya kuma nemi a kai masa dukkan kwafe-kwafen takardun biyan kuɗaɗen da aka ce an yi.

Kwamitin bincike ya kuma nemi a kai masa sunayen dukkan kamfanonin da aka taɓa biya kuɗaɗen tallafin fetur da adadin da aka riƙa biyan kowane.

Wannan tashin-balli ya zo ne bayan Minista Zainab ta bayyana cewa Najeriya na buƙatar naira tiriliyan 6.7 domin ta biya tallafin fetur da kuɗaɗen.

Aliyu ya ce wannan lamari abin damuwa ne matuƙa.

“Dole Minista ta bayyana domin gabatar da bayanai masu damun ‘yan Najeriya. Ciki har da shirin da gwamnati ke yi domin ciwo bashi a biya tallafin fetur da kuɗaɗen bashin.

Wanan binkice na faruwa ne makonni biyu bayan Minista Zainab ta ce tattalin arzikin Najeriya ya kusa durƙushewa; an gano saura dala biliyan 15 a asusun waje, ba dala biliyan 36 da CBN ya ce saura ba.

Yayin da Najeriya ke shirin zaɓen 2023 cikin shekara mai zuwa, hujjoji na ƙara bayyana cewa tattalin arzikin ƙasar fuskantar matsanancin yanayi biyu: wato baitilmalin da ba ko ranyo a ciki, sai kuma raguwar da tattalin ke yi a kullum.

Jami’an gwamnati da manyan ‘yan kasuwar da ke da masaniyar halin da ake ciki, sun ce ana nuna damuwa sosai a Abuja da Legas, yayin da wani zaɓaɓɓen jami’in gwamnati ya jawo hankalin Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele cewa abin da ya rage a asusun Najeriya da ke waje fa bai wuce dala biliyan 15 ba, wato ƙasa sosai da dala biliyan 36 ɗin CBN ɗin ya yi iƙirarin cewa su na cikin asusun.

Yayin da Najeriya ta kashe naira tiriliyan 5.9 wajen shigo da kayayyaki daga waje tsakanin Janairu zuwa Afrilu 2022 kaɗai, dala biliyan 15 kacal ɗin ƙasar ke da shi a yanzu ba su wuce kashewa cikin watanni huɗu kacal ba kenan wajen shigo da kayayyaki.

Masana harkokin tasarifin kuɗaɗen sun ce da a ce komai na tafiya daidai, to raguwar kuɗaɗen ba abin damuwa ba ne. Amma abin fargabar shi ne yadda aka shafe watanni shida cur Najeriya ba ta zuba ko sisi a cikin asusun don kuɗin su ƙaru ba. Wannan kuma ya faru ne saboda matsalar rashin wadatar ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa waje ne, da kuma tsayuwar gwanin jakin da kasuwar ta yi.

Sannan kuma ɗaukar lokaci mai tsawo da NNPC ta yi ta kada zuba cinikin ɗanyen mai a CBN, shi ne ya haifar da tsawwala farashin dala a kasuwannin ‘yan canji.

Wata babbar ma’aikaciyar banki wadda ta ce wannan jarida ta rufa mata asiri kada ta ambaci sunan ta, ta ce an daɗe ana ɓoye gaskiyar sauran adadin kuɗaɗen gwamnati a cikin asusun waje, wanda babbar matsala ce sosai a halin yanzu.

Ta ce an yi ƙarin gishiri ne wajen ainihin yawan kuɗaɗen da ke CBN, domin kawai a ɓoye ainihin adadin da su ka rage a asusun waje.

An haƙƙaƙe cewa wannan babban jami’in gwamnati wanda kuma zaɓen sa aka yi, ya sanar wa Shugaba Muhammadu Buhari gaskiyar halin da ake ciki na ramewar tattalin arzikin Najeriya. Sai dai kuma Fadar Shugaban Ƙasa ba ta amsa wa PREMIUM TIMES tambayoyin da ta yi kan wannan mawuyacin halin da ake ciki ba.

Sannan kuma maida NNPC hannun jarin masu kasuwanci da aka ce an yi, ya ƙara dagula matsalolin. Wato tunda NNPC ya kasa zuba kuɗaɗen cinikin ɗanyen mai ko na fetur a asusun CBN, tilas kenan bankin ya tashi ya inda zai samu manyan kuɗaɗen ƙasashen waje.

Abin damuwa a nan shi ne, mafi yawan hanyoyin da CBN zai iya samun kuɗaɗen duk a toshe su ke da majinar murar da ta toshe hancin CBN ɗin, wanda kuma shi da kan sa ya ƙirƙiri tsarin da ya haifar da toshewar ƙofofin hancin na sa.

Ma’ana dai tunda asusun ajiyar kuɗaɗe na waje an kasa saka masa komai tsawon watanni huɗu, to ƙasar nan ba ta da sukunin iya biyan kuɗaɗen abinci, magunguna da kayan ayyuka daban-daban da ake buƙatar shigo da su a masana’antun mu. Wato dai irin matsalar tattalin arzikin da Sri Lanka ke fuskanta a yanzu kenan.

Maganar dai kai tsaye ita ce Najeriya na fuskantar mummunar matsalar ƙarancin kuɗi, ga wawakeken giɓin kasafin kuɗi, tulin basussuka da kuma taguwar da kuɗaɗen shigar da ƙasar ke samu ke yi a kullum.

Cikin Yuli PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda matsalar ƙarancin kuɗaɗe ta yi wa Najeriya rumfa inda a cikin watannin Janairu zuwa Afrilu kuɗaɗen da ƙasar ta biya bashi, sun haura kuɗaɗen shigar da ta samu a cikin waɗancan watannin huɗu.

Kafin NNPC ta kasa ci gaba da zuba kuɗin cinikin ɗanyen mai a CBN, a duk wata ta kan zuba dala biliyan 3 daga ɗanyen man da Najeriya ta sayar a watan. Amma kuma kusan shekara ɗaya kenan NNPC ba ta zuba abin da ya kai ko da dala miliyan 200 ba.

Cikin watan jiya ne Ministan Ƙwadago Chris Ngige ya ce a kwantar da hankali tare da yin taka-tsantsan, saboda fatara da talauci sun yi wa Najeriya tarnaƙi da dabaibayi. Ta kai babu kuɗaɗen da ƙasar za ta biya manyan ayyukan raya ƙasa a shekara mai zuwa. Hakan na nufin lamarin zai ƙara munana matsalar rashin aikin yin da ake fama da ita, sai kuma ƙaruwar malejin ƙuncin rayuwa da hakan zai haifar kenan a shekara mai zuwa.

Cikin makon juya ne kuma Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed ta ce Gwamnatin Tarayya ta kamfaci dala biliyan 1 daga Asusun Rarar Kuɗin Fetur, domin inganta tsaro.

Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta kwashi naira biliyan 1 daga Asusun Rarar Kuɗin Fetur (ECA), domin inganta harkokin tsaro, a daidai lokacin da kuɗaɗen shiga daga fetur ke ƙara raguwa sosai.

Zainab ta yi wannan bayani a gaban manema labarai, ranar Laraba, a fadar Shugaban Ƙasa, ƙarshen zaman su da Shugaba Muhammadu Buhari.

Waɗannan kuɗaɗe da Zainab ta ce an kamfata, lamarin ya zo ne daidai lokacin da ake kukan cewa kuɗaɗen asusun sun ragu sosai da sosai.

Rahotanni sun ce kuɗaɗen da ke cikin asusun sun ragu daga dala miliyan 35.7 a cikin Yuni 2022 zuwa dala 376,65.09 a ranar 25 Ga Yuli, 2022.

Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito cewa Akanta Janar ne ya bayyana sauran adadin a ranar Talata, amma bai faɗi dalilin raguwar kuɗaɗen ba.

A ranar Laraba dai Minista Zainab ta ce wutsilniyar da kasuwar ɗanyen mai ke yi a duniya ce ta tankwafe asusun har kuɗaɗen su ka ragu.

“Tsawon shekaru huɗu kenan ba mu saka ko sisi a cikin Asusun Rarar Ribar Fetur ba, saboda faɗi-tashin da kasuwar ɗanyen mai ke yi a duniya.” Inji Zainab.

“To abin da mu ke da shi a cikin asusun ne mu ka riƙa cira a hankali ana yin wasu ayyuka da su. Kuma duk lokacin da za a yi amfani da kuɗaɗen, sai an nemi shawarar Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa, wato gwamnoni, saboda asusu ne na Gwamantin Tarayya.

“Kuɗin da aka cira daga asusun a baya-bayan nan, su ne dala biliyan 1 domin a inganta harkokin tsaro. Kuma duk abin da ake cira sai da sanin Gwamnoni.”

Tags: AbujaHausaMajalisar TarayyaMinistar KuɗaɗeNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Ina nan da rai na cikin koshin lafiya gadagau – Kabiru Nakwango

Next Post

Wawanci da shashanci ke sa wasu na kwaikwayon tangaɗi, rangaji da karkarwar hannun Tinubu -Sanatan PDP

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
ZAƁEN FIDDA-GWANIN APC: Yadda bishiyoyin da Tinubu ya shuka shekarun baya su ka yi masa inuwa a 2022

Wawanci da shashanci ke sa wasu na kwaikwayon tangaɗi, rangaji da karkarwar hannun Tinubu -Sanatan PDP

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Kotun Amurka ta amince Jami’ar Jihar Chicago na iya jinkirta sakin bayanan karatun Tinubu
  • JAMI’AR GUSAU: Ba tun yau bane ƴan ta’adda ke yi wa ɗaliban jami’ar ɗauki ɗaiɗai
  • ƘALUBALE GA MATAWALLE DA BADARU: Sace Ɗaliban Jami’ar Gusau da Dawowar Ta’addanci a Arewa Maso Yamma, Daga Ahmed Ilallah
  • Wike ya soke lasisin mallakar filayen wasu jigajigan Najeriya ciki har da Peter Obi
  • Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.