Yayin da rashin jituwa tsakanin Gwamna Nysome Wike na Jihar Ribas ke ƙara haifar da ɓaraka tsakanin sa da ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP Atiku Abubakar, Gwamnonin PDP sun kai masa ziyara a ranar Lahadi.
Gwamnonin sun kai ziyarar ce kwana ɗaya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, Yakubu Dogara da Babachir Lawal sun kai masa ziyara, jim kaɗan bayan dawowar sa daga bulaguro a ƙasar waje.
Gwamnonin da su ka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi su ka gana da shi a asirce, a Gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro, Abuja.
Ba a san dai abin da su ka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da saɓanin da ke ƙara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.
An samu saɓani tsakanin manyan jiga-jigan PDP ɗin biyu, tun bayan kammala zaɓen fidda-gwani, inda Atiku ya yi nasara, shi kuma Wike ya zo na biyu.
Tun bayan kammala zaɓen dai Wike ya yi tsinuwa da Allah–wadai ga wasu manyan jam’iyyar da ya ce sun yi masa butulci, inda ake ganin da Gwamna Aminu Tambuwal ya ke, wanda ya janye kafin zaɓe, ya ce a zaɓi Atiku.
Wike ya kuma ragargaji masu zaɓen ‘yan takara daga Kudu, waɗanda ya ce sun sayar da ‘yancin ‘yan kudu saboda ‘yan kuɗi kaɗan.
Sannan kuma Wike ya ragargaji ɗaukar Gwamna Okowa na Jihar Delta matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa ga Atiku.
Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaɓe, ya bi Wike ɗin har gida ya ba shi haƙuri. Kuma ya ce shi zai ɗauka mataiakin takara.
Ɗaukar Okowa ya fusata Wike, inda ya riƙa fesa wa Atiku munanan kalamai, kuma har yau bai taya Okowa murnar zama ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na PDP ba.
Kwanan nan Atiku ya fito ya ce masu ba shi shawarar wanda zai ɗauka mataimakin takara, ba su ba shi sunan Wike ba. Wannan furuci daga Atiku ya harzuƙa Wike, har ya kira Atiku ƙasurgumin maƙaryaci.
Gwamnonin da su ka ziyarci Wike sun haɗa da: Seyi Makinde na Oyo, Samuel Ortom na Benuwai, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.
Tsoffin gwamnonin sun haɗa da Donald Duke na Cross River, Gabriel Suswan na Benuwai, Olusegun Mimiko na Ondo, Ibrahim Idris na Kogi da Johan Jang na Filato.
Jiga-jigan PDP sun fara ɗar-ɗar da Wike tun bayan da gwamnonin APC uku daga Kudu maso Yamma su ka kai masa ziyara. Sai kuma ziyarar da Yakubu Dogara da Babachir Lawal su ka kai masa a ranar Asabar.
An ruwaito Wike dai na cewa ba zai fita daga PDP ba.
Discussion about this post