Kotun majistare dake Ikeja jihar Legas ta bada belin wasu mata biyu da suka ci zarafin ‘yar shekara biyu akan Naira 200,000 kowannen su.
Alkalin kotun B. O. Osunsanmi wacce ta dage shari’ar zuwa ranar 26 ga Satumba sannan kuma ta ce kowace mace za ta gabatar da shaida daya a zama ta gaba da kotun za ta yi.
Osunsanmi ta yanke wannan hukunci ne bayan an kama malaman makaranta mai zaman kansa dake Obanikoro, Deborah Babajide mai shekara 42 dake lamba 4D layin Akinlabake dake rukunin gidajen Akerele a Oworonshoki sannan da Toyin Odusanya wacce ke kula da yara kananan na makarantar mai shekara 48 kuma take zaune a gida mai lamba 10 layin Abajada dake Oworonshoki da laifin saka hannu a gaban ‘yar shekara biyu.
Dan sandan da ya shigar da karan ASP Raji Akeem ya ce matan sun aikata wannan mummunar abu ne ranar 6 ga watan Mayu a Obanikoro.
Akeem ya ce mahaifiyar yarinyar ce ta kawo kara ofishinsu bayan ta ga rauni a gaban ‘yarta.
“Mahaifiyar ta ce ta lura idan tana yi wa ‘yarta wanka sai yarinyar ta rika nuna jin zafi musamman idan ana wanke gaban ta.
“Ta ce daga dubawa sai ta ga rauni da alamun cewa an taba gaban ta.
” Daga nan ne fa sai yarinyar ta bayyana wa mahaifiyar ta cewa Aunty ne ta taba ta.
Ya ce a dalilin haka rundunar ta kama malamar da matar dake kula da yara kanana na makarantar.
A kotun Deborah da Toyin sun musanta aikata laifin da kotun ke zarginsu da shi.
Discussion about this post