Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta bada tabbacin cewa ta damƙe sojoji biyu da ake zargin su da hannu wajen kashe fitaccen malamin addinin Musulunci mai suna Sheikh Goni Gashuwa.
An kashe Sheikh Goni ne a ranar Juma’a da dare bayan ya wuce Nguru.
Kakakin Yaɗa Labarai na Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe, Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da cewa waɗanda ake zargi da kisan malamin sojoji ne guda biyu, kuma tuni su na hannun ‘yan sanda.
Sai dai kuma ya ce lokaci bai yi ba da za a yi gaggawar fitar da bayanai tukunna.
“Da zaran an natsa wajen bincike cikin ‘yan kwanaki za a sanar da komai.
Sai dai kuma rundunar ‘yan sandan ta Yobe ba ta bayyana sunayen sojojin da aka kama ba.
Majiya ta ce farkon lamarin dai wani soja ne ya tsayar da Sheikh Goni bayan ya wuce Nguru.
“Bayan ya wuce Nguru ne kuma sai ya tsaya domin ya yi fitsari. Bayan Sheikh da gama ya nufi mota, sai sojan ya nuna shi da bindiga, ya ce idan ya matsa zai harbe shi. Kuma nan take ya harbe shi.
“Bayan sojan ya bindige malamin, sai ya nemi tayar da motar malamin ya gudu, amma mota ta ƙi tashi. Daga nan ne kuma ya kira soja na biyu.
“Da soja na biyu ya zo ne, sai suka ga ashe motar ma ta ci karan-shaf. Sai su ka kira ‘yan bijilante don su je su taya su kiciniya.
“Ana cikin kiciniyar motocin biyu ne, sai ‘yan bijilante su ka ga ɗaya motar da jini a jikin ta. Bayan sun duba sai su ka ga gawar Sheikh Goni a cikin daji. Daga baya su ka kai rahoto wurin ‘yan sanda.”
Mataimakin Sufurtandan ‘Yan Sanda kuma Kakakin su na Jihar Yobe, Dungus Abdulkarim, ya ce sun amsa laifin da ake tuhuma.
Ya dai ce za a bayyana komai idan an kammala bincike.
Wannan ne karo na uku da haka ta faru da jami’an tsaro a Jihar Yobe.
Discussion about this post