Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP Atiku Abubakar da Gwamna Nyesom Wike sun amince cewa kowa a cikin su zai bayar da sunayen mutum bakwai, domin a kafa kwamitin da zai shata sharuɗɗan daidaitawar ɓangarorin biyu.
An cimma wannan yarjejeniyar ce a taron da Atiku da Wike su ka yi ranar Juma’a, a gidan Jerry Gana, a Abuja.
Wannan ne karo na farko da manyan masu rashin jituwar a PDP su ka haɗu, tun bayan kammala zaɓen fidda-gwanin ‘yan takarar PDP, wanda Atiku ya zo na farko, Wike ya zo na biyu.
PREMIUM TIMES dai ta tabbatar cewa nan cikin sa’o’i 48 aka ce za a kafa kwamitin, amma ba ta tabbatar da sunayen da Atiku ya bayar ba, ko kuma sunayen da shi ma Wike ya bayar a kwamitin ba.
An tuntuɓi Kakakin Yaɗa Labaran Atiku, Paul Ibe, amma bai maido amsa ba.
Sharuɗɗan Da Wike Ke So A Cika Kafin A Sasanta:
A makon jiya ne dai Kwamitin Amintattu ya kafa wani kwamitin zaman sulhu da Wike.
Kwamitin Amintattun PDP ya kafa wani kwamitin zama domin ganawa da hasalallun cikin jam’iyya.
Wasu daga cikin waɗanda kwamitin zai zauna da su, sun haɗa da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da kuma wasu manyan jam’iyya masu goyon bayan sa da kuma masu fushi da fushin Wike.
Shugaban Kwamitin Amintattu ko kuma a ce Kwamitin Dattawa, Walid Jibrin, ya bayyana wa manema labarai a ranar Laraba cewa an kafa kwamitin bayan wani dogon zama na sa’o’i biyu da dattawan jam’iyyyar su ka yi.
Ya ce dukkan mambobin kwamitin su na cikin wannan sabon kwamitin da aka kafa, a matsayin masu shiga tsakani domin a sasanta.
“Mun kafa kwamitin ne domin a samu sulhun rashin jituwar da ke tsakanin ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar da Gwamna Nyesom Wike, kai da ma duk wani mai wani ƙullaci da ƙulafuci a cikin zuciyar sa a cikin PDP.”
Sai dai kuma Jibrin bai faɗi tsawon lokacin da kwamitin zai ɗauka ya na aikin sasancin ba.
Da aka tambaye shi ko sun tattauna batun neman saukar Shugaban PDP Iyorchia Ayu da su Wike ɗin su ka jajirce cewa sai dai ya sauka? Sai Jibrin ya ce wannan ba wani abin tattaunawa ba ne, kuma ba su tattauna a kan hakan ba.
Kafa wannan kwamiti ya zo ne cikin gaggawa, kwana ɗaya bayan Wike da magoya bayan sa sun yi wata ganawar da su ka yi gagarimin shirin sa ƙarar wando ɗaya da Atiku.
kwana ɗaya bayan da manyan ‘yan tawayen APC, Yakubu Dogara da Babachir Lawal sun kai masa ziyara, jim kaɗan bayan dawowar sa daga bulaguro a ƙasar waje.
Gwamnonin da su ka kai wa Wike ziyara, sun je ne tare da wasu tsoffin gwamnonin PDP, inda a ranar Lahadi su ka gana da shi a asirce, a Gidan Gwamnatin Jihar Ribas da ke Asokoro, Abuja.
Ba a san dai abin da su ka tattauna ba. Amma kuma tabbas tattaunawar ba ta rasa nasaba da saɓanin da ke ƙara tsanani tsakanin Wike da Atiku Abubakar.
An samu saɓani tsakanin manyan jiga-jigan PDP ɗin biyu, tun bayan kammala zaɓen fidda-gwani, inda Atiku ya yi nasara, shi kuma Wike ya zo na biyu.
Tun bayan kammala zaɓen dai Wike ya yi tsinuwa da Allah–wadai ga wasu manyan jam’iyyar da ya ce sun yi masa butulci, inda ake ganin da Gwamna Aminu Tambuwal ya ke, wanda ya janye kafin zaɓe, ya ce a zaɓi Atiku.
Wike ya kuma ragargaji masu zaɓen ‘yan takara daga Kudu, waɗanda ya ce sun sayar da ‘yancin ‘yan kudu saboda ‘yan kuɗi kaɗan.
Sannan kuma Wike ya ragargaji ɗaukar Gwamna Okowa na Jihar Delta matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa ga Atiku.
Daga baya Wike ya ce Atiku ya yaudare shi, domin bayan kammala zaɓe, ya bi Wike ɗin har gida ya ba shi haƙuri. Kuma ya ce shi zai ɗauka mataiakin takara.
Ɗaukar Okowa ya fusata Wike, inda ya riƙa fesa wa Atiku munanan kalamai, kuma har yau bai taya Okowa murnar zama ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na PDP ba.
Kwanan nan Atiku ya fito ya ce masu ba shi shawarar wanda zai ɗauka mataimakin takara, ba su ba shi sunan Wike ba. Wannan furuci daga Atiku ya harzuƙa Wike, har ya kira Atiku ƙasurgumin maƙaryaci.
Gwamnonin da su ka ziyarci Wike sun haɗa da: Seyi Makinde na Oyo, Samuel Ortom na Benuwai, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.
Tsoffin gwamnonin sun haɗa da Donald Duke na Cross River, Gabriel Suswan na Benuwai, Olusegun Mimiko na Ondo, Ibrahim Idris na Kogi da Johan Jang na Filato.
Discussion about this post