Kasar Najeriya da a ke ganin tafi kowace kasa girman tattatalin arziki a Africa, ita tafi kowace kasa karancin albashi a jamióin su.
Nigeria fa ita ce kasar da yayan ta suka fi fita kasashen waje neman yin karatun Jamiá a fadin Africa. A kalla kowace shekara suna kasha kudin da ya kai sama da Naira B100, abin takaici mafi yawan wannan kudade suna zuwa kasashen da basu kai Nigeria irin su Benin, Ghana Uganda.
Najeriya tana da yawan Jami’a 217, a cikin wannan jam’oi guda 45 ne kawai mallakar gwamnatina, guda 57 mallakar gwamnatin jahohi sannan kuma guda 111 masu zaman kansu ne.
A yau a kwai kimanin matasa kusan miliyan biyu da suke karatu a jami’oin Nijeriya, banda kusan rabin miliyan da suka zauna jarabawar JAMB suna jiran dakun shiga jami’a.
Yanzu dai a kalla yan ASUU da sauran ma’aikatan Jami’a sun shafe sama da watanni 5 suna yajin aiki, a takaice jami’o in Nijeriya suna gargame, yara dalibai suna gida. Kuma tamkar babu ranar komawa makaranta, domin babu alamun samun daidaito tsakanin gwamnati da ASUU da sauran ma’aikatan jami’oin Nigeria. Wadan nan kinshikai guda 5 sune za su hana sassanawa a kan lokaci.
MUHIMMANCIN ILIMI A WAJEN SHUGABANNIN NIJERIYA:
A yau dukkanin ƴan Nijeriya za su iya bawa kan su amsa a kan irin muhimmancin shugabannin Nijeriya suka bawa ilimi a kowane mataki daga karamar hukuma, jahohi da ita kanta tarayyar. Kowa yasan yanayin da makarantun gwamnati na firamare da sakandare suke ciki, daga rashin ingancin malamai, kayan aiki da yanayin da makarantun suke ciki. Shin wane irin muhimmanci shugabanni suka bawa wadannan makarantu.
Duk a cikin halin da ake ciki na yajin aikin malaman jami’o in Nijeriya da sauran ma’aikatan jami’a bai hana shugabannin Nijeriya yin bikin yaye nasu yayan ba a jami’oin kasashen waje, duk da cewar suna ta ihun Nijeriya tana cikin talauchi. Tamkar wannan yajin aikin su bai shafe suba da yayan su.
Inda shugabannin Nijeriya sun damu da halin da ilimi yake ciki a Nijeriya da ko sati biyu baza a yi ba ana wannan yajin aikin.
2009 AGREEMENT DA MALLAKAR JAMI’A A NIJERIYA:
A cikin dalilan shigar ASUU da sauran ma’aikatan jamiá shiga yajin aiki akwai bukatar aiwatar da yarjejeniyar 2009, wanda a cikin wannan yarjejeniya a kwai sabunta albashin ma’aikatan a duk bayan shekaru 4, wanda tunda a kayi wannan yarjejeniya, gwamnati bata taba aiwatar waba, a wannan karon yan ASUU sunce baza su koma ba sai an aiwatar da wannan yarjejeniya.
Gwamanti a wannan karon ta kafa kwamiti karkashin Professor Briggs, wanda ya amince da karawa malaman jami’a kashi 109 zuwa kashi 180, wanda daga baya gwamnati tace sai ta sake duba a kan wanna rahoton kwamatin. Domin in har ta amince da wanna rahoto, to ko shakka babu sai gwamnati ta kara kimanin N360B akan albashin da take biyan malaman jami’a, wanda take ganin haka da wahala ya iyu, ganin yanayin da tattalin arikin kasar ke ciki. A na jitajitar cewa gwamantin kan iya aminata da abin da bai wuce kashi 100, ko da an aminta da hakan Nijeriya mafi karancin albashin ma’aikatan Jami’a a Africa.
Kamar yadda na fada a sama a Nijeriya a kwai kimanin Jami’o I guda 217, wanda gwamnatin tarayya guda 45 kadai ta mallaka sauran kuma na jahohi ne da masu zaman kansu ne.
Kowa ne mataki gwamnatin tarayya ta aminta da shi, sun nuna cewa baza su amincewa jahohi ba, saboda basu san karfin jahohi ba wajen wajen biyan albashin ba, domin jahohi suna da yancin cin gashin kansu, amma su shugabbanin ASUU sunce kungiyar ta hada harda jami’an jahohi. Koda an samu sasanto, shin jahohi zasu iya aminta.
BABU HADIN KAI TSAKANIN MINISTOCIN BUHARI:
Takon sakar da ya bayyana karara tsakanin Shi kansa Ministan Ilimi da takwaran sa na kwadago, zai iya kawo jan kafa a kan yin sasanton, tun farko Ministan Kwadago yace hakkin Hukumar Ilimce take da hakkin yin sasanto da ma’aikatanta, har sai abin ya ci tira ne hukumar kwadago zasu shiga, wanda wannan ya haifar da kafa kwamitin Prof. Briggs.
Amma daga baya munji ruhotannin suna fitowa daga fadar Shugaban Kasa cewa, shi ministan kwadago ne ya cewa majalissar zartarwa cewa hukumar sa ce mai hakin yin sasanto irin wannan, amma fa har tsawon wata biyar sun kasa sasanta wa a tsakanin su.
A sati uku da suka gabata kuma wani ruhotin ya fito cewa Shugaba Buhari ya bawa Minstan Ilimi sati biyu a kan ya kawo karshen yajin aikin a cikin sati biyu, kuma ya cire hannun Ministan Kwadago a ciki, amma fa har yau babu wani ci gaba da a ka samu, babu ma wani labara mai dadi a kan wannan matsalar.
RASHIN TSARIN SASANTO TSAKANIN MA’AIKATA DA HUKUMOMI:
Duk da kasancewar a kwai dokoki da suka shafi kwadago da kuma tsarin da ya kamata abi in har a ka gaza samun sasanto tsakanin ma’aikata da hukumomin da su ke yiwa aiki, amma su kan su hukumomin basu cika son a na zuwa hukumomin ba irin su Labour Dispute Arbitrary Panel ko Industrial Court ba, wanna bai wuce cewar hukomin ne basu da gaskiya a irin wannan rigimar ba.
IPPIS, UTAS DA UPS3:
Tun a shekara ta 2020 ASUU da ma’aikatan jami’a suka ki aminta da shiga tsarin biyan albashi ta hanyar da gwamnati ta samar ta IPPIS, bisa dalilan su na cewa ba zai yi da dai da irin tsarin aikin jami’a ba, har sai da suka tafi yajin aiki na tsawan wata 9 a kan wannna matsalar.
ASUU sun yi nuni ta yadda a ke zambar gwamnati biliyoyin kudade ta wannan manjhajar.
Shin zargin da a ke yiwa tsohon Babban Accountant kasar nan na yin almundaha na ta wannan manhajar zata sa gwamnati ta sake tunani a kan wannan tsarin, ko zargin d ASUU ta yi zai iya zama gaskiya.
Wadanna suna da ga cikin dalilan da yi wa sassanto gwamnati da ma’aikatan Jami’a tarnakin sasantawa, domin yaron mu su koma kararatu.
Allah ya kauta.
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post