Mazaunan kauyen Morai dake karamar hukumar Talata Mafara sun bayyana cewa a ranar Litinin da safe ‘yan bindiga sun kashe mutum hudu a kauyen sannan sun yi garkuwa da mutum 30 daga wannan kauyen.
Mazaunan sun ce maharan sun afka kauyen da misalin karfe 02:30 na dare suka yi ta tafka barna suna cin karen su ba babbaka har zuwa karfe 6 na safe.
Wani mazaunin kauyen Mansur Zainu ya ce wannan shine karon farko da mahara suka kawo hari wannan kauyen
Zainu ya ce maharan sun kashe mutum hudu a kauyen inda a ciki akwai wani dan karamin yaro, Sarkin Fawa Sani Na’Ayi da Wani dan kasuwa Yahaya Mohammed.
Kanen Yahaya Mohammed wanda maharan suka kashe da baya so a fadi sunan sa ya ce matar mamacin, kawunsa da kanwar matar mamacin na daga cikin mutanen da maharan suka yi garkuwa da su.
“A lokacin da maharan suka afka kauyen Mohammed shi ya fara rugawa waje daga cikin gidansa amma da ya ga ba zai iya tsere wa maharan ba sai ya boye a bayan wani rumbu. Ashe wani dan bindigan ya ga inda ya boye inda ya bi bayan sa ya harbe shi a Kai har sau biyu.
Wani mazaunin Lawal Suyidi ya ce mafi yawan mutanen da maharan suka yi garkuwa da su mata ne.
“A cikin gidan mu kawai mata hudu da kanne na biyu maza suka yi awon gaba da.
“Mun daina kirga yawan mutanen da suka bace domin wasu sun dawo gida ranar Litini da yamma. Duk da haka mun samu mutum 30 da basu a gidajen su.
Discussion about this post