Sanatan da ya taba gaura wa wata mata mari a shagon siyar da azzakarin roba, Sanata Elisha Abbo ya bayyana ficewa daga tafiyar Bola Tinubu Dan takarar shugaban kasa na APC, saboda ya zabi musulmi dan takarar mataimakin sa a zaben shugaban kasa mai zuwa.
Abbo ya ce Tinubu bai kyauta wa Kiristocin Najeriya ba duk da wasiku da suka aika masa na ya tabbata ya zabi kirista ne mataimakinsa amma kuma kirikiri ya yi abinda ya ga dama.
” Tinubu bai kyauta ba da ya zabi siyasar sa gaba da zamantakewar yan Najeriya, tsintsiya daya madauri daya.
” Mun yi taro a Abuja muka aika masa da sakon cewa kada ya kuskura ya zabi musulmi a matsayin mataimakin sa amma yayi mana kunnen uwar shegu yayi wancakali da umarnin mu. A matsayina na jigo a kungiyar kiristoci CAN, ba zan zabi siyasa gaba da addini na ba.
” Za mu hakura da tafiyar Tinubu tunda ya zabi musulmi, mu kiristoci ba za mu yi tafiyar sa ba. Zan zabi abinda ya fi dacewa kasar mu ne ba siyasar zaben ‘yan addini daya su yi takara ba.
A karshe Abbo ya ce ba takarar musulmi da musulmi ba kawai, ko kirista da kirista ne ba zai amince ba.
Discussion about this post