Sanata Uba Sani wanda shine dan takarar gwamnan jihar Kaduna na jam’iyyar APC ya yi kurin cewa ko tantama ba shi da shi cewa dan takarar shugaban Kasa na APC ne zai lashe jihar Kaduna a zaben shugaban kasa da za a yi a 2023.
” Ina so ku dau takarda ku rubuta, ku ce nine na fadi, a jihar Kaduna Tinubu da Kashim Shettima ne za su kwankwadi madarar kuri’un mutanen Kaduna. Kuma ina tabbatar muku cewa za ku fadi na ce haka bayan zabe ina so ku shaida haka.
Uba ya kara da cewa mutane na yi wa gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai shiga sharo ba shanu, su na yanke hukunci a kansa a bubuwan da basu sani ba, bayan kuma ba haka bane.
” Ina son in gaya wa duniya cewa shugaban mu kuma gwamnan mu mai adalci, Nasir El-Rufai ne ya fara kokarin kiran Kashim Shettima bayan Tinubu ya bayyana shi a matsayin dan takarar mataimakin shugaban Kasa na jam’iyyar APC. Amma kuma makiya da masu hassada suka garzaya wasu kafafen yada labarai suka rika kantara masa karya, suna fadin wani abu daba haka ba.
” El-Rufai na tare da wannan zabi sannan yana tare da Tinubu 100 bis 100.
Bayan haka sai sanata Uba Sani ya kaddamar da Kashim Shettima shugaban kungiyar Matan Arewa masoya Tinubu wanda a wurin wannan taro ya kwarzanta Shettima da tinubu da yi musu alkawarin lallai za su yi aiki tukuri=u wajen ganin su ne suka yi nasara a jihar Kaduna idan zabe ya zo.
Discussion about this post