Kotun majistare dake jihar Kaduna ta gurfanar da Ibironke Taiye mai shekara 35 bisa laifin damfarar abokinsa naira miliyan 3.5.
A ranar Talata alkalin kotun Ibrahim Emmanuel ya bada belin Taiye akan naira 500,000.
Emmanuel ya ce Taiye sai gabatar da shaidu biyu ‘yan uwansa dake aiki, mazaunan jihar Kaduna ne dake biyan gwamnatin jihar haraji.
Ya ce za a ci gaba da shari’a ranar 24 ga Agusta.
Dan sandan da ya shigar da karar Chidi Leo ya ce ‘yan sanda sun kama Taiye dake zama a layin Ethopia dake Barnawa Kaduna da laifin sata da damfara.
Leo ya ce Taiye ya aikata haka ne tun a shekarar 2021 a Keke 2 Millennium City dake Kaduna inda ya damfari abokinsa Donald Vincent naira miliyan 3.5.
“Taiye ya yi wa abokinsa Vincent tallar filin sa fegi daya da rabi dake Millennium City akan naira miliyan 3.5.
“Tun da Taiye ya karbi kudaden daga hannun Vincenta ya gudu ya bar gari ba tare da ya nuna wa Vincent filin ba.
“Bayan Vincent ya shigar da kara a ofishin ‘yan sanda ne muka gano cewa Taiye ya damfani abokinsa da filin da bashi da shi.
Leo ya ce sun yi farautan Taiye Kuma sun kama shi a jihar a Legas.
Discussion about this post