Aƙalla maniyya 1,238 masu tafiya aikin Hajjin bana daga Jihar Kano na fuskantar yiwuwar rasa samun damar tafiya Hajjin 2022, idan ba a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki ba.
Saboda saura sa’o’i kaɗan a rufe filin jirgin saman Jeddah.
Mahukuntan Saudi Arabiya sun bayyana cewa za su rufe sararin samaniyar ƙasar a ranar Laraba, 6 Ga Yuli, 2022 domin fara shirye-shiryen aikin Hajji gadan-gadan.
Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihar Kano, Muhammad Ɗambatta, ya ce rashin maniyyatan Kano na ƙasa ba a kwashe su ba, duk kuwa da cewa ana jajibirin rufe sararin samaniyar Saudi Arebiya.
Maniyyatan na fuskantar matsalolin tashin jirage, saboda har zuwa yau maniyyata 1,075 kaɗai daga cikin 2,313 aka ɗauka daga filin jirgin saman Kano.
Wani malamin Jami’a Adams Abdullahi ya zargi Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) da haifar da tangarɗar ga Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.
“Mutanen fa ba su jin daɗin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, saboda fatali da kamfanin jiragen sama na Azman ɗan jihar Kano.
An samu tangarɗa saboda an ƙi amincewa yin mu’amala da kamfanin da ya yi rajista da Bankin Jaiz Bank cikin harkokin Hajiin 2022.
Ya ce ba za a ɗauke shi ba a ƙyale kamfanonin da su ka yi rajista tun daga 20219, 2020 da 2022 a ƙarƙashin Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.” Inji Malamin Jami’ar Bayero.
“Ta yaya NAHCON za su ƙirƙiro wata ƙa’idar da za ta yi sanadiyyar daga ɗimbin maniyyata su rasa tafiya aikin Hajjin da su ke ta fatan zuwa shekara da shekaru?
Ya yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya shiga lamarin ta umartar NAHCON su samar wa maniyyatan Kano babban jirgin da zai yi saurin kwashe su, kafin a rufe sararin samaniyar Saudi Arabiya a ranar Laraba.
Shi kuma Ɗambatta ya ce Hukumar Kula da Jin Daɗin Alhazan Kano na nan na ƙoƙarin tabbatar da ta samu jirgin da zai kwashe maniyyatan kafin a rufe filin jirgin Jeddah.
Ya zargi NAHCON da bai wa Kano jirgin Azman, wanda ba ya da manyan jiragen ɗaukar fasinja masu yawa sosai.
“Jirgin Azman na ɗaukar fasinjoji 100 ne kacal zuwa Saudi Arabiya. Kuma jirgin su na shafe awa shida daga Kano kafin ya kai Jeddah, maimakon awa huɗu kacal.
“Sun yi jigila sau biyar, amma har yanzu ko rabin fasinjojin ba su kwashe ba.”
Ita kuwa NAHCON ta sha alwashin cewa ba za a bar kowane maniyyaci a ƙasa ya na hajijiya ba.
Discussion about this post