Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan ya bayyana cewa babu yadda za a yi a kai wannan mummunan hari a Gidan Kurkukun Abuja ba tare da haɗin baki da wasu jami’an kula da gidajen kurkuku ba.
Da ya ke nuna damuwa da gazawar tsaro kuwa, Lawan ya yi jawabi a fusace bayan an kewaya da shi ya ga irin ɓarnar da aka yi, inda ya ce maganar gaskiya ɓangaren tsaro a Najeriya ya gaza kawai.
“Harin da Boko Haram su ka kai a Kirkiro Kuje ranar Talata alama ce da hujjar da ke nuna cewa kakaf tsarin tsaro a Najeriya a durƙushe ya, ya gaza kawai.”
Kalaman Lawan sun zo daidai lokacin da Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola ya ce an kai harin duk kuwa da cewa akwai ɗimbin dakarun tsaro kewaye da kurkukun.
A lokacin da Lawan ya kai ziyara a ranar Alhamis, ya yi iƙirarin cewa, “kai irin wannan mummunan hari ba zai yiwu ba tare da hannun wasu jami’an kula da kurkuku ba.”
Daga nan ya nuna ɓacin rai saboda ji da ganin da ya yi na yadda Hukumar Kula da Kurkuku ta Ƙasa ba ta da Kyamara Mai Fallasa Mugaye (CCTV) a Kurkukun Kuje da sauran kurkukun faɗin ƙasar nan.
Jawabin da Lawan ya yi na cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labaran sa Ezrel Tabiowo ya fitar bayan kammala ziyarar.
Lawan ya jagoranci tawagar Shugabannin Majalisar Dattawa, domin gane wa idon su irin munin ɓarnar da mahara su ka yi a kurkukun.
Babban Kwanturolan Gidajen Kurkuku na Ƙasa, Haliru Nababa ne ya kewaya da shi ciki da wajen kurkukun.
Ya yi kira da a saka kuɗaɗen CCTV a cikin Kasafin 2023, domin a sa kyamarorin fallasa mugaye a dukkan kurkukun ƙasar nan.
PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda ISWAP su ka raba wa ɗaurarrun da su ka arce daga Kurkukun Kuje Naira 2,000 kowa ya yi kuɗin mota zuwa gida.
Mazauna garin Kuje, musamman waɗanda ke kusa da kuma bayan kurkukun da aka kai wa hari, sun bayyana wa wakilin mu yadda lamarin ya faru, wanda su ka ce ba su fatan su ga maimaicin wani abu mai kama da haka.
Farmakin wanda aka kai a ranar Talata, ya yi sanadiyyar arcewar ɗaurarru 800 daga cikin mutum 994 da ke tsare su a ciki.
Sai dai kuma jami’an kurkukun sun ce an kamo 442, amma kuma har yanzu babu labarin sauran 443 da su ka tsere.
Wani maƙaucin kurkukun mai suna Micheal, ya shaida wa wakilin mu cewa maharan aƙalla za su kai 100.
Ya ce ba garkiya ba ne da gwamnati ta ce kimanin minti 30 maharan suka yi.
“Gaskiya sun fi awa biyu a kurkukun. Saboda tun ƙarfe 9 na dare su ka dira, kuma 11 su na wurin.
“Ni ina ƙofar gida tare da wani aboki na, mu na shirin hawa babur mu je wani wuri, wajen ƙarfe 9 na dare, kawai sai mu ka fara jin ƙara da rugugi. Ni da farko na yi zaton ko nakiya ce ake fasawa ma. Wannan ƙarar rokoki ne da aka riƙa harbawa don a fasa bangon kurkukun.”
Micheal ya ce da ya ga abin ba na wasa ba ne, ya dafe ƙeya ya shiga gida a guje.
“Na nufi gida a guje. Wani soja daga cikin waɗanda ke gadin kurkukun ya biyo ne shi ma a guje, mu ka runtuma mu ka afka cikin gida. Sojan nan ya yi sauri ya cire yinifom ɗin sa. Mu ka shige ƙarƙashin gado.”
“Bindigogin da maharan ke amfani da ita, manya ne sosai, kuma da harsasai kawai ke fita, ba ƙaƙƙautawa.”
Wani kuma da aka zanta da shi, ya ce sun ga yadda ɗaurarru su ka riƙa fita su na tserewa.
“Wasu ma tafiyar taƙama su ke yi abin su. Wasu kuma gudu wasu sauri.
“Maharan sun riƙa raba wa waɗanda su ka tsere ɗin kowane naira 2,000 domi ya yi kuɗin mota. Wani wanda ya kasa tafiya ne da ya ga ba zai iya ba, wataƙila saboda rauni, ya shaida mana haka. Har ma ya yi ƙoƙarin maida naira 2,000 ɗin da ya ce an ba shi.”
Ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa maharan sun tsallako rafi ne su ka kai harin.
Discussion about this post