Duk da tsananin hare-haren kare dangi da ƴan bindiga suka kai wa dakaru, fasa gidan uarin kuje, da harin tawagar sa a Katsina, shugaban kasa Muhammadu Buhari zai waske zuwa Dakar yau Laraba.
Idan ba a manta ba shi kansa shugaba Buhari bai tsira daga harin ƴan bindiga ba inda a ranar Talata suka yi wa tawagar jami’an tsaron sa da suka yi gaba zuwa Daura kwantan ɓauna suka.
Bayan haka kuma a cikin daren Talata ƴan Boko Haram suka fasa gidan yarin Kuje daje Abuja suka saki fursunonin sama da 300 dake tsare a gidan.
Duk da irin wannan rashin zaman lafiya da hare-hare da suka yi tsanani, shugaba Barack hari zai garzaya Dakar domin halartar taro.
Ministar kuɗi, Zainab Ahmed, Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emiefile, da wasu jigajigan gwamnati ne za su raka Buhari.
Sanarwar ta ce Buhari zai dawo ranar Alhamis 7 ga wata.