Sama da shekaru 10 kenan Jihar Zamfara ta samu kan ta cikin ruɗanin ‘yan bindiga masu kashe-kashen jama’a su na fyaɗe da garkuwa da mutane da banka wa ƙauyuka wuta. Matasa ne masu ɗauke da bindigogi ƙirar AK47 su na shiga ƙauyuka da tare hanyoyi su na garkuwa da mutane a cikin surƙuƙin daji domin karɓar kuɗin fansa.
An kashe dubban mutane kuma kusan mutum miliyan ɗaya sun rasa muhalli, sun zama ‘yan gudun hijirar ƙarfi da yaji.
Wannan tashin hankali bai bar ƙananan yara ba. Da ya ke akwai haɗari ga ‘yan jarida su riƙa shiga cikin ƙauyuka don ganin abin da ake ciki, sai dai kullum a riƙa samun kanun labarai a jaridu.
A ƙoƙarin da BBC Afraca Eye ya Yi domin sani da ganin takamaimen abin da ke faruwa, shirin ya shafe sama da shekaru biyu ya na bibiya tare da zantawa da wasu gagga kuma hatsabiban ‘yan bindigar Zamfara.
Shirin ya yi ƙoƙarin gano amsoshin wasu tambayoyin da aka kasa gano amsoshin na su: Su wane waɗannan ‘yan bindiga? Me su ke so ne? Me ya sa wannan rikici ya samo asali ne?
A ƙoƙarin gano waɗannan amsoshi, wani matashi kuma ɗalibin da ke karatun lauya mai suna Yusuf Anka, ya ziyarci Shugabannin waɗannan ‘yan bindiga a cikin surƙuƙin jejin jihar Zamfara. Cikin su har da waɗanda su ka yi garkuwa da ɗaliban sakandaren Jangebe a watan Fabrairu, 2021.
Anka ya tattaro bayanai masu firgitarwa a ganawar da ya yi da masu garkuwar da waɗanda aka yi garkuwar da su ko waɗanda tashen-tashen hankulan ya shafe su.
Sai dai me, za a iya cewa duk da akwai jami’an tsaro, Gwamnatin Najeriya ta kasa samar da tsaro ga ɗimbin ‘yan ƙasar ta. Kuma binciken da Anka ya yi, ya nuna yadda aka maida garkuwa da karɓar kuɗaɗen fansa wata babbar hanyar samun maƙudan kuɗaɗe. Haka kuma rikice-rikicin ya nuna akwai ɓurɓushin rikicin ƙabilanci tsakanin Hausawa da Fulani.
‘Bindigogi Mu Ke Saye’:
‘Yan bindigar da su ka saci ɗalibai mata sama da 300 a Jangebe babu wanda ya taɓa kama ko ɗaya daga cikin su. Kuma a baya ba su taɓa hira da kowace jarida ba. Amma tawagar BBC ta ritsa ɗaya daga cikin gogarman da su ka jagoranci kai harin kama ɗaliban a cikin makarantar su.
Ya yarda an ɗauki bidiyon tattaunawar da aka yi da shi, inda ya ce an biya ‘yan bindigar naira miliyan 60. Kuma Gwamantin Najeriya ce ta biya kuɗin aka saki yaran mata.
“To ku me ku ke yi da kuɗin?” Anka ya yi masu wannan tambaya, inda ya ce “Bindigogi mu ka ƙara sayowa da su.”
Sai dai kuma a koyaushe Gwamnatin Zamfara musanta cewa an biya kuɗin fansar wasu da aka ceto.
Bidiyon ya kuma yi rikodin ɗin yadda aka maida yaran wurin iyayen su a cikin watan Maris, 2021.
“Ni Aiki Na Kisa Kawai” -Ada Aleru
Cikin tattaunawar wadda ita kaɗai ce Aleru ya taɓa yi, gogarman wanda Gwamnatin Jihar Katsina ke nema ruwa jallo, kuma wanda aka naɗa Sarkin Fulanin ‘Yandoto a kwanan nan a Zamfara, an tambaye shi ko mutum nawa ya kashe, sai ya ce, “Yara ke zuwa su kamo, ni kashewa kaɗai na ke yi.”
Wani makusancin Aleru ya bayyana baƙin cikin da ya ce ke sa matasa Fulani ke shiga ta’addancin kisa da garkuwa da mutane. Ya yi kukan rashin burtali da wuraren kiwon shanu hatta ruwan da dabbobi za su sha ya yi ƙaranci.
Kuma ya yi ƙorafin yadda ƙiri-ƙiri aka ture Fulani daga shiga cikin ayyukan gwamnati da sauran damammakin inganta rayuwar su. Kuma sojojin sama na karkashe Fulani makiyaya waɗanda ba ‘yan bindiga ba ne. “Kawai an maida rayukan Fulani ba a bakin komai ya ke ba.” Inji shi.
A cikin faifan bidiyon, akwai batutuwa da dama da aka tattauna, ciki kuwa har da yadda rikicin ya zamo faɗa tsakanin Hausawa ‘yan sakai da Fulani da kuma yadda fitinar ta hana Hausawa walwala, musamman sukunin zuwa gona noma, kamar dai yadda rikicin ya hana Fulani shiga cikin gari domin yin hidimomin kawar da lalurorin yau da kullum.
Discussion about this post