• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Ba mu da masaniyar ɗaukar tsohon ɗan Boko Haram aikin tsaron gidan kurkuku -Babban Kwanturolan Kurkuku

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 14, 2022
in Labarai
0
KWANAKI 100 BAYAN HARIN JIRGIN ƘASAN ABUJA: Yadda Boko Haram su ka ruguza Kurkukun Abuja, su ka ƙwaci dakarun su 64 da ke tsare

Shugaban Hukumar Kula da Gidajen Kurkuku na Ƙasa, Haliru Nababa, ya bayyana cewa ba shi da masaniyar an ɗauki tsohon ɗan Boko Haram aikin tsaron gidajen kurkuku.

Tsohon ɗan Boko Haram ɗin da ake magana dai shi ne Wilberforce Yohanna, wanda Premium Times ce ta buga labarin ɗaukar na sa a labaran jaridar na makon jiya.

Nababa ya yi wannan iƙirarin na rashin sanin ɗaukar Yohanna, a lokacin da ake tattaunawa da shi a shafin Tiwitar, wanda PREMIUM TIMES ce ta shirya tattaunawar.

An yi tattaunawar ce kan makomar biyo bayan Boko Haram ɓangaren ISWAP sun kai wa Kurkukun Abuja da ke Kuje.

Kwanturolan Kurkuku ya ce ba a sanar da shi cewa Yohanna, wanda ke da lambar ɗauka aiki ta ‘Mataimakin Jam’i (Assistant Cadre) ASC11 da ke aiki Gidan Kurkukun Yola cewa tsohon ɗan Boko Haram ba ne, har sai da ya karanta binciken da PREMIUM TIMES ta buga.

Sai dai kuma ya ce Hukumar Kula da Gidajen Kurkuku ta Ƙasa ta kafa kwamitin binciken lamarin.

“Wato gaskiyar magana ba a kawo min wani abu mai kama da ɗaukar tsohon ɗan Boko Haram ba.” Inji shi.

Duk da Haliru ya ce ba a sanar da shi ba, amma kuma PREMIUM TIMES ya samu kwafen wata takardar gargaɗi wadda ta riƙa yawo a cikin hukumar mai ɗauke da cewa an fa gano Yohanna tsohon ɗan Boko Haram ne.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga Rahoton Musamman, kan yadda aka bankaɗo tsohon ɗan Boko Haram ya zama Jami’in Gidan Kurkuku, watanni biyar kafin farmakin Kurkukun Kuje. Amma kuma mahukuntan hukumar su ka binne maganar, har sai da wannan jarida ta fallasa, sannan maganar ta fito fili.

Ga Labarin Nan:

Mai barci ya tashi, na tsaye ya zauna, mai tafiya ya dakata ya sha labarin yadda tsohon ɗan Boko Haram ya zama ma’aikacin tsaro a gidan kurkuku, wanda aiki ne gwamnatin tarayya ke ɗauka.

Ranar 18 Ga Fabrairun da ya wuce ne balli ya tashi a Sabon Gidan Kurkukun Yola a Jihar Adamawa, inda aka gano cewa a cikin sabbin ma’aikatan kurkukun, har da wani gwanin iya harbi da sarrafa manyan bindigogi mai suna Wilberforce Yohanna.

Hankalin manyan jami’an kurkukun ya tashi da su ka gano cewa Yohanna tsohon ɗan Boko Haram ne.

Wasu sahihan bayanan sirri da Hukumar Kula da Gidajen Kurkuku ta rubuta dangane da Yohanna, sun faɗo hannun PREMIUM TIMES, wadda bayan ta tabbatar da lamarin, buga labarin ya zama wajibi.

Yadda Aka Gano Yohanna Tsohon Ɗan Boko Haram Ne:

An gano Yohanna tsohon ɗan Boko Haram ne tun a wurin bada horo ga sabbin-yanka-raken da ake ɗauka, inda aka je koya masu yadda ake sarrafa bindiga ƙarama da babba.

Jami’an bayar da horo sun lura ko a cikin su babu wanda ya kai Yohanna iya sarrafa bindiga ƙarama ko babba. Iya loda harsasai da hanzari a cikin ƙwarewa, ba a fi shi iyawa ba, sai dai ya koyar, amma ba a koya masa ba.

Yohanna ya zama abin kallo ga jami’an bayar da horo ganin yadda ya ke yi wa bindiga filla-filla, ya kuma haɗa ta a cikin ƙwarewa. Tun a wajen riƙe bindiga babba da ƙarama aka fahimci Yohanna da wani gogarma ne.

An tafi da shi wajen masu bincike, inda bayan an sheƙa masa ruwan tambayoyi, sai ya faɗa masu cewa a gaskiya shi fa tsohon ɗan Boko Haram ne.

Yohanna ya shaida masu cewa amma shi ba aƙidar Boko Haram ya ke da ita ba. Ya yi iƙirarin cewa kama shi ‘yan Boko Haram su ka yi, su ka kuma tilasta shi ɗaukar makami ya taya su yaƙin tsawon shekaru biyu. Daga baya ne ya ya samu wata dama da sa’a, ya tsere, ya kuɓuta daga hannun su. A cewar sa fa.

Sai dai kuma ba a tantance ba shin bayanin yadda ya shiga Boko Haram ɗin da ya yi gaskiya ne, ko kuma ya danne gaskiyar, ƙarya kawai ya yi?

An ɗauki Yonanna aikin kula da kurkuku watanni biyar kafin Boko Haram su kai wa Kurkukun Kuje mummunan harin da har su ka kuɓutar da ‘yan uwan su 64 da kuma haddasa arcewar ɗaurarru fiye da 400.

Majiya daga kurkukun ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa lamarin Yohanna ya zame wa Hukumar Kula da Kurkukun Najeriya alaƙaƙai. Ga shi dai an samu tantagaryar ɗan Boko Haram a cikin su, amma ba a son ɗaga murya don kada ‘yan jarida su yi labari su watsa duniya.

Binciken da PREMIUM TIMES ta yi a cikin jami’an da su ka nemi a ɓoye sunan su, sun tabbatar da cewa, irin birkitaccen tsarin da ake bi idan za a ɗauki sabbin jami’an kurkuku, lalataccen tsari ne, wanda kuɗi kawai mai neman aiki zai biya a ɗauke shi aikin.

“Ba a maganar cancanta, kawai iyar kuɗin ka iyar shagalin ka. Wanda za a ɗauka a matakin Level 8 na ma’aikacin gwamnatin tarayya, zai biya naira 800,000. Matakai na zuwa na ƙasa kuwa a kan biya naira 400,000 ko sama da haka.” Inji wata majiya da ta ce shi ya sa mai laifi ba zai yi wahalar samun shiga aikin jami’an tsaron kurkuku a Najeriya ba.

Idan ba a manta ba, tsohon Gwamnan Jihar Yobe, Sanata Ibrahim Geidam ne ya bijiro da ƙudirin yafe wa tubabbun Boko Haram, a Majalisar Dattawa, kuma aka amince har ƙudirin ya zama doka cikin 2020.

Bayan ƙudirin ya zama doka, an kafa Hukumar Yi Wa Tubabbun Boko Haram Wankin Kankarar Mummunar Aƙida, Koya Masu Sana’o’i da Maida Su Cikin Jama’a.

Sai dai kuma mutane da dama sun riƙa kushe wannan shiri, su na cewa wasu ba tuba su ke yi ba, su na komawa daji wurin Boko Haram duk su kwashi bayanan sirri su kai wa kwamandojin Boko Haram.

Yayin da al’ummar da tubabbun ‘yan Boko Haram ɗin su ka fito cikin su ke ƙyamar sake zama tare da su, Gwamna Babagana Zulum na Barno ya taɓa cewa shirin tarairayar tubabbun ‘yan Boko Haram ɗin ba shi da fa’ida, domin wasun su daji su ke komawa su sake ɗaukar makami.

Sannan kuma za a iya tunawa a ranar Alhamis ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan ya yi iƙirarin cewa shi ya na ganin da haɗin bakin wasu jami’an kurkuku Boko Haram su ka fasa kurkukun Kuje.

PREMIUM TIMES ta tuntuɓi Kakakin Yaɗa Labaran Hukumar Kula da Kurkukun Najeriya, Abubakar Umar, wanda ya ce labarin ɗaukar tsohon ɗan Boko Haram aikin tsaron kurkuku ba gaskiya ba ne, ƙarya ce.

Sai dai kuma PREMIUM TIMES ta gano cewa shi ma ɗin bai faɗi gaskiya ba, domin labarin ɗaukar Yohanna aiki ya bazu sosai a cikin manya da ƙananan jami’an Hukumar Kula da Gidajen Kurkukun Najeriya.

Tags: AbujaHausaKurkukuNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Kungiyar NUPENG ta yi wa Ƙungiyar Ƙwadago mubaya’ar shiga zanga-zanga saboda rufe jami’o’i

Next Post

TATTAUNAWA: Budurwar gefe na dauke wa namiji tunane-tunane. Lalacewa ne mai aure ya ajiye budurwar gefe – Inji Mazajen aure a Zaria

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Man and Woman

TATTAUNAWA: Budurwar gefe na dauke wa namiji tunane-tunane. Lalacewa ne mai aure ya ajiye budurwar gefe - Inji Mazajen aure a Zaria

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Ruhun Mai Tsarki ne ya umarce ni na kashe ta’ – Inji matar da ta kashe ‘yar shekara biyar
  • RIGA MALAM MASALLACI: Matasan Kano sun yi wa ginin ƴan canji diran mikiya, sun yi warwason kayan ‘ganima’
  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin jari mai kauri ya sa noma na ya ƙi gaba, ya ƙi baya – Wata mace mai himma
  • CIRE TALLAFIN MAI: Kungiyoyin ma’aikatan lantarki, Ƴan jarida da na Kwadago za su tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba
  • Yadda bashin Dala Miliyan 19.3 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.