• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

    ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC

    An kama Sanata Ekweremadu da matar sa a Landan, bisa zargin yunƙurin cire ƙodar wani ƙaramin yaro

    2023: APC ta ƙara wa’adin ranakun zaɓen fidda ‘yan takarar gwamna, sanata da na wakilan jihohi da tarayya

    KOWAR HAƊIYI TAƁARYA: Shugaban APC ya gana da Sanatocin APC domin magance fitar-farin-ɗango da ake yi daga jam’iyyar

    RAHOTO: Akalla ‘ƴan Najeriya miliyan 48 ne ke ƙantara kashi ‘bahaya’ a waje

    RAHOTO: Akalla ‘ƴan Najeriya miliyan 48 ne ke ƙantara kashi ‘bahaya’ a waje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

    ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC

    An kama Sanata Ekweremadu da matar sa a Landan, bisa zargin yunƙurin cire ƙodar wani ƙaramin yaro

    2023: APC ta ƙara wa’adin ranakun zaɓen fidda ‘yan takarar gwamna, sanata da na wakilan jihohi da tarayya

    KOWAR HAƊIYI TAƁARYA: Shugaban APC ya gana da Sanatocin APC domin magance fitar-farin-ɗango da ake yi daga jam’iyyar

    RAHOTO: Akalla ‘ƴan Najeriya miliyan 48 ne ke ƙantara kashi ‘bahaya’ a waje

    RAHOTO: Akalla ‘ƴan Najeriya miliyan 48 ne ke ƙantara kashi ‘bahaya’ a waje

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TSAKANIN OSINBAJO DA TINUBU: Wa Zai Ci Riba, Wa Zai Yi Asarar Jari Da Uwar Kuɗi A Zaɓen Fidda gwani?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 7, 2022
in Ra'ayi
0
Tsarin shugabanci a wurin Tinubu baiwa ce – Inji Osinbajo

Kokawa ce tsakanin yaro da ubangidan sa, amma ta zama ta mutum biyar, har da wasu ‘yan takara uku. Amma dai wannan nazari ya maida hankali kan mutum biyu.

PREMIUM TIMES Hausa ta sake binciko wani nazari da ta yi wa manyan ‘yan takarar shugaban ƙasa biyu a ƙarƙashin APC.

Nazarin ya yi daidai da sakamakon yadda Taron Gangamin APC na yau Talata zuwa gobe Laraba zai haifar.

Fitowar Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo takarar shugaban ƙasa na zaɓen 2023 a ƙarƙashin APC, jam’iyya ɗaya da ubangidan sa Bola Tinubu, hakan ya nuna za a yi kokawa kenen tsakanin yaro da ubangida.

Akwai jan aiki sosai wurjanjan a gaban Osinbajo, wanda idan bai hana idanun sa barci ba, zai sha kayen tsiya a hannun Tinubu, ko dai da ƙarfin kuɗi, ko ƙarfin faɗa-a-ji, tunda Tinubu na da yara gwamnoni tsoffi da masu ci, tsoffin ministoci da waɗanda ke kan karaga, ko kuma ƙarfin ‘yan jagaliya.

Tashin farko za a ga cewa daga cikin gwamnonin APC 23, 12 kaɗai su ka halarci taron sa na ranar Lahadi, inda bayan an yi buɗa-baki ya bayyana masu niyyar sa ta fitowa takara.

Babbar matsalar da Osinbajo zai fuskanta kuma ita ce ta tsantsar ra’ayin sa na fifita mabiya Ɗariƙar ‘Pentacostal’, ‘yan Cocin RCCG a rabon muƙamai. Wannan halayyar ta sa na yi wa su kan su sauran Kiristoci ciwo.

Akasarin manyan muƙaman da Osinbajo ya yi hanya aka naɗa, duk mabiya Ɗariƙar da ya ke bi ne, ‘yan Cocin RCCG. Kakakin Yaɗa Labaran Osinbajo Laolu Akande, ɗan Cocin RCCG ne, kuma fasto ne a cocin na birnin New York, Amurka. Ya dawo Najeriya da aka ci zaɓen 2015, ya zama Kakakin Yaɗa Labaran Osinbajo.

A cikin Ministocin Buhari na 2015 zuwa 2019, Osinbajo ya bayar da sunan Okechukwu Enelameh aka naɗa shi Ministan Cinikayya, Kasuwanci, Masana’antu da Zuba Jari (2015-2019). Shi ma fasto ne a Cocin RCCG.

RCCG na nufin Redeemed Christian Church of God.

Wasu ɓangaren Musulmi na jin haushin Osinbajo, ganin yadda a rayuwar sa Musulmai ne su ka cicciɓa shi har ya hau kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa, amma kuma sai ya riƙa maida hankali wajen naɗa ‘yan Ɗariƙar Cocin RCCG a manyan muƙaman gwamnati.

Osinbajo ya bayar da sunan faston RCCG, Babarunde Fowler aka naɗa shi Shugaban Hukumar Tara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida (FIRS), wanda ya shekara biyar sannan aka cire shi aka naɗa wani.

Musulmi Lauya kuma tsohon Ministan Shari’a, Bola Ajibola ne ubangidan Osinbajo na farko, kafin wani Musulmin, Bola Tinubu.

Kafin Tinubu, Yemi Osinbajo ya yi Hadimin Musamman a Ofishin Lauya na kamfanin Bola Ajibola.

Duk da ɗan asalin Jihar Ogun ne, hakan bai hana Bola Tinubu naɗa shi Kwamishinan Shari’a na Jihar Lagos ba, tsakanin 1999 zuwa 2007.

Kada a manta Osinbajo ya yi koyarwa a Jami’ar Legas.

Yayin da aka zo neman wanda za a naɗa Shugaban Hukumar BPE, an bai wa Osinbajo damar kawo wanda ya cancanta, inda ya bayar da sunan fasto Alex Ayoola-Okoh, ɗan Ɗarikar RCCG, ta su Osinbajo ɗin.

Haka Shuagaban Bankin Masana’antu (BOI), wanda Osinbajo ne sanadin naɗa shi, wato Olukayode Pitan, shi ma faston RCCG ne.

Ba waɗannan ne kaɗai ‘yan Cocin RCCG da Osinbajo ya yi wa hanya su ka samu manyan muƙamai ba.

Kada kuma a manta, a cikin 2016, watan Nuwamba, jaridar Vanguard ta ruwaito Osinbajo na cewa, “Tinubu ne ya bada suna na aka naɗa ni ɗan Takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa a APC.”

Ko ma dai me kenan, alamomi sun nuna cewa Osinbajo ya fara gane cewa waɗannan halayyar da ya nuna a baya za su iya zame masa matsala a zaɓe ko a zaɓen fidda gwani. Ba mamaki mai yiwuwa dalili kenan ya fara jawo Musulmai a jika, ta hanyar ɗaukar nauyin tafsirin watan azumi a wasu gidajen radiyo.

Sannan kuma kiran gwamnonin APC taron shan ruwa a ranar Lahadi da ta gabata, shi ma wata hanya ce ta fara sakin ra’ayin sa na riƙau kan Ɗarikar RCCG.

Shi ma ubangidan sa Tinubu akwai ƙalubalen matsalolin da zai fuskanta sosai. Na farko farfagandar cewa tsoho ne tukub ta yi mummunan tasiri a ƙoƙarin sa na neman a tsaida shi takara a APC.

Masu amfani da wannan farfaganda na cewa kada wani tsoho ya sauka, kuma a maye gurbin sa da wani tsohon.

Sannan kuma an riƙa yaɗa cewa shi ma ko ya hau, a Landan zai riƙa zirga-zirgar fita neman magani ko ganin likitocin sa, ya na farin ‘yan Najeriya cikin mawuyacin hali.

Matsalar motoci biyu masu sulke ɗauke da maƙudan kuɗaɗe a jajibirin zaɓen 2019 daga banki har cikin gidan Tinubu, ta sa an riƙa tanganta shi tamkar wani samfurin maguɗin zaɓe.

Kari da cewa ana raɗe-raɗin zai ɗauki Gwamna Abdullahi na Jihar Kano a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa, ya sa Tinubu ba zai iya yin tasiri a Arewa ba, sai dai idan ƙarfa-ƙarfa ko hajijiya za a yi ranar zaɓe.

Ana yi wa Ganduje kallon wanda ya yi ƙarfa-ƙarfar cin zaɓe a 2019 a ‘incoclusive’ na Mazaɓar Gama, cikin Ƙaramar Hukumar Nasarawa.

Sannan kuma bidiyon da ake zargin ya na danna dalolin toshiyar baki a cikin aljifan sa, har yau ba su fice daga ƙwaƙwalen ɗimbin jama’a ba, duk kuwa da an raɗa wa Ganduje suna Khadimul Islam.

Kada a yi mamakin kokawar neman takara tsakanin Tinubu da Osinbajo. Mulki ya gaji har ɗa ya yi wa uban sa juyin mulki. Hakan ba sabon abu ba ne. Ballantana kuma kokawar yaro da ubangida.

Ai dama Bahaushe ya ce, “na kawo ƙarfi ya fi wane ya girme ni.”

Tags: AbujaLabaraiNewsOsinbajoPREMIUM TIMES
Previous Post

BA A HANA WANDA BAI YARDA BA YA SHIGA TAKARA: Gwamnonin APC da Kwamitin Gudanarwa sun fitar da ‘yan takara 5, sun zubar da 17

Next Post

ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

Next Post
ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari
  • Ƴan bindiga sun yi garkuwa da jami’an lafiya uku da mace mai ciki a Zamfara
  • SHIRYE-SHIRYEN ZAƁEN 2023: INEC ta yi wa ƙarin mutum fiye da miliyan 10 rajista
  • SUN CI TALIYAR ƘARSHE: Sanatoci 58 da ba za su koma Majalisar Dattawa a zaɓen 2023 ba
  • INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.