• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TSAKANIN OSINBAJO DA TINUBU: Wa Zai Ci Riba, Wa Zai Yi Asarar Jari Da Uwar Kuɗi A Zaɓen Fidda gwani?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 7, 2022
in Ra'ayi
0
Tsarin shugabanci a wurin Tinubu baiwa ce – Inji Osinbajo

Kokawa ce tsakanin yaro da ubangidan sa, amma ta zama ta mutum biyar, har da wasu ‘yan takara uku. Amma dai wannan nazari ya maida hankali kan mutum biyu.

PREMIUM TIMES Hausa ta sake binciko wani nazari da ta yi wa manyan ‘yan takarar shugaban ƙasa biyu a ƙarƙashin APC.

Nazarin ya yi daidai da sakamakon yadda Taron Gangamin APC na yau Talata zuwa gobe Laraba zai haifar.

Fitowar Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo takarar shugaban ƙasa na zaɓen 2023 a ƙarƙashin APC, jam’iyya ɗaya da ubangidan sa Bola Tinubu, hakan ya nuna za a yi kokawa kenen tsakanin yaro da ubangida.

Akwai jan aiki sosai wurjanjan a gaban Osinbajo, wanda idan bai hana idanun sa barci ba, zai sha kayen tsiya a hannun Tinubu, ko dai da ƙarfin kuɗi, ko ƙarfin faɗa-a-ji, tunda Tinubu na da yara gwamnoni tsoffi da masu ci, tsoffin ministoci da waɗanda ke kan karaga, ko kuma ƙarfin ‘yan jagaliya.

Tashin farko za a ga cewa daga cikin gwamnonin APC 23, 12 kaɗai su ka halarci taron sa na ranar Lahadi, inda bayan an yi buɗa-baki ya bayyana masu niyyar sa ta fitowa takara.

Babbar matsalar da Osinbajo zai fuskanta kuma ita ce ta tsantsar ra’ayin sa na fifita mabiya Ɗariƙar ‘Pentacostal’, ‘yan Cocin RCCG a rabon muƙamai. Wannan halayyar ta sa na yi wa su kan su sauran Kiristoci ciwo.

Akasarin manyan muƙaman da Osinbajo ya yi hanya aka naɗa, duk mabiya Ɗariƙar da ya ke bi ne, ‘yan Cocin RCCG. Kakakin Yaɗa Labaran Osinbajo Laolu Akande, ɗan Cocin RCCG ne, kuma fasto ne a cocin na birnin New York, Amurka. Ya dawo Najeriya da aka ci zaɓen 2015, ya zama Kakakin Yaɗa Labaran Osinbajo.

A cikin Ministocin Buhari na 2015 zuwa 2019, Osinbajo ya bayar da sunan Okechukwu Enelameh aka naɗa shi Ministan Cinikayya, Kasuwanci, Masana’antu da Zuba Jari (2015-2019). Shi ma fasto ne a Cocin RCCG.

RCCG na nufin Redeemed Christian Church of God.

Wasu ɓangaren Musulmi na jin haushin Osinbajo, ganin yadda a rayuwar sa Musulmai ne su ka cicciɓa shi har ya hau kujerar Mataimakin Shugaban Ƙasa, amma kuma sai ya riƙa maida hankali wajen naɗa ‘yan Ɗariƙar Cocin RCCG a manyan muƙaman gwamnati.

Osinbajo ya bayar da sunan faston RCCG, Babarunde Fowler aka naɗa shi Shugaban Hukumar Tara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida (FIRS), wanda ya shekara biyar sannan aka cire shi aka naɗa wani.

Musulmi Lauya kuma tsohon Ministan Shari’a, Bola Ajibola ne ubangidan Osinbajo na farko, kafin wani Musulmin, Bola Tinubu.

Kafin Tinubu, Yemi Osinbajo ya yi Hadimin Musamman a Ofishin Lauya na kamfanin Bola Ajibola.

Duk da ɗan asalin Jihar Ogun ne, hakan bai hana Bola Tinubu naɗa shi Kwamishinan Shari’a na Jihar Lagos ba, tsakanin 1999 zuwa 2007.

Kada a manta Osinbajo ya yi koyarwa a Jami’ar Legas.

Yayin da aka zo neman wanda za a naɗa Shugaban Hukumar BPE, an bai wa Osinbajo damar kawo wanda ya cancanta, inda ya bayar da sunan fasto Alex Ayoola-Okoh, ɗan Ɗarikar RCCG, ta su Osinbajo ɗin.

Haka Shuagaban Bankin Masana’antu (BOI), wanda Osinbajo ne sanadin naɗa shi, wato Olukayode Pitan, shi ma faston RCCG ne.

Ba waɗannan ne kaɗai ‘yan Cocin RCCG da Osinbajo ya yi wa hanya su ka samu manyan muƙamai ba.

Kada kuma a manta, a cikin 2016, watan Nuwamba, jaridar Vanguard ta ruwaito Osinbajo na cewa, “Tinubu ne ya bada suna na aka naɗa ni ɗan Takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa a APC.”

Ko ma dai me kenan, alamomi sun nuna cewa Osinbajo ya fara gane cewa waɗannan halayyar da ya nuna a baya za su iya zame masa matsala a zaɓe ko a zaɓen fidda gwani. Ba mamaki mai yiwuwa dalili kenan ya fara jawo Musulmai a jika, ta hanyar ɗaukar nauyin tafsirin watan azumi a wasu gidajen radiyo.

Sannan kuma kiran gwamnonin APC taron shan ruwa a ranar Lahadi da ta gabata, shi ma wata hanya ce ta fara sakin ra’ayin sa na riƙau kan Ɗarikar RCCG.

Shi ma ubangidan sa Tinubu akwai ƙalubalen matsalolin da zai fuskanta sosai. Na farko farfagandar cewa tsoho ne tukub ta yi mummunan tasiri a ƙoƙarin sa na neman a tsaida shi takara a APC.

Masu amfani da wannan farfaganda na cewa kada wani tsoho ya sauka, kuma a maye gurbin sa da wani tsohon.

Sannan kuma an riƙa yaɗa cewa shi ma ko ya hau, a Landan zai riƙa zirga-zirgar fita neman magani ko ganin likitocin sa, ya na farin ‘yan Najeriya cikin mawuyacin hali.

Matsalar motoci biyu masu sulke ɗauke da maƙudan kuɗaɗe a jajibirin zaɓen 2019 daga banki har cikin gidan Tinubu, ta sa an riƙa tanganta shi tamkar wani samfurin maguɗin zaɓe.

Kari da cewa ana raɗe-raɗin zai ɗauki Gwamna Abdullahi na Jihar Kano a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa, ya sa Tinubu ba zai iya yin tasiri a Arewa ba, sai dai idan ƙarfa-ƙarfa ko hajijiya za a yi ranar zaɓe.

Ana yi wa Ganduje kallon wanda ya yi ƙarfa-ƙarfar cin zaɓe a 2019 a ‘incoclusive’ na Mazaɓar Gama, cikin Ƙaramar Hukumar Nasarawa.

Sannan kuma bidiyon da ake zargin ya na danna dalolin toshiyar baki a cikin aljifan sa, har yau ba su fice daga ƙwaƙwalen ɗimbin jama’a ba, duk kuwa da an raɗa wa Ganduje suna Khadimul Islam.

Kada a yi mamakin kokawar neman takara tsakanin Tinubu da Osinbajo. Mulki ya gaji har ɗa ya yi wa uban sa juyin mulki. Hakan ba sabon abu ba ne. Ballantana kuma kokawar yaro da ubangida.

Ai dama Bahaushe ya ce, “na kawo ƙarfi ya fi wane ya girme ni.”

Tags: AbujaLabaraiNewsOsinbajoPREMIUM TIMES
Previous Post

BA A HANA WANDA BAI YARDA BA YA SHIGA TAKARA: Gwamnonin APC da Kwamitin Gudanarwa sun fitar da ‘yan takara 5, sun zubar da 17

Next Post

ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

ƘAREWAR KWANA: Daliget daga Jigawa ya rasu a daidai yana karin kumallo a Abuja

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad
  • SHARI’AR ZABEN SHUGABAN ƘASA: Kotu ta karɓi sakamakon zaɓen jihohi 17 daga hannun Peter Obi domin tantance sahihancin su
  • TSAKANIN ATIKU DA KEYAMO: Keyamo ya ɗaukaka ƙarar hukuncin tarar Naira Miliyan 10 da Kotun Tarayya ta danƙara masa
  • KOTUN ZAƁEN SHUGABAN ƘASA TA ƊAU ZAFI: Yadda Atiku ya kaɗa hantar Tinubu, APC da INEC a zaman shari’ar ranar Laraba
  • Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.