Jam”iyyar APC na neman dagulewa sanadiyyar kasa samun yadda za ta fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa, wanda zai iya goyayya da Atiku Abubakar, wanda PDP ta tsayar tun a farkon makon jiya.
Yayin da Gwamnonin Arewa 12 na APC su ka amince a bai wa ɗan Kudu takarar, shi kuma Abdullahi Adamu ya fito ya ce sun yarda a bar wa Sanata Ahmad Lawan takarar.
Su dai Gwamnonin APC sun jaddada amincewa a bai wa Kudu takara a wurin ganawar su da Shugaba Muhammadu Buhari, ranar Litinin, kwanaki biyu kafin ranar zaɓe.
Gwamnan Filato Simon Lalong ne ya bayyana wa manema labarai wannan matsaya ta gwamnonin Arewa, bayan sun fito daga ganawa da Buhari, a cikin Fadar Shugaban Ƙasa.
Gwamna Nasiru El-Rufai ya bayyana cewa daga cikin gwamnonin APC 14 na Arewa, Gwamna Yahaya Bello na Kogi ne kaɗai bai amince a bai wa Kudu su fito da ɗan takarar shugaban ƙasa na APC ba.
Tun a ranar Asabar aka riƙa yayata cewa Buhari ya amince a bai wa Kudu takara, labarin da Kakakin Yaɗa Labaran Buhari, Garba Shehu ya ƙaryata.
Tuni dai Shugabancin Jam’iyyar APC su ka ƙi amincewa da kalamai da su ka fito daga Adamu cewa an naɗa Ahmad Lawan ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa.
Har Yanzu Buhari Bai Yanke Shawarar Miƙa Takara Ga Ɗan Kudu Kai-tsaye Ba -Gwamna Badaru:
Gwamna Abubakar Badaru na Jigawa ya ce har yanzu gwamnonin APC na Arewa na jiran Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana matsayar sa kan miƙa takarar shugaban ƙasa ga ɗan kudu kai-tsaye.
Badaru ya bayyana haka a cikin wata tattaunawar da ya yi da BBC Hausa a ranar Lahadi.
A ranar Asabar ce dai Gwamnonin APC na Arewa da masu faɗa-a-ji na jam’iyyar daga Arewa, su ka amince mulki ya koma kudu a zaɓen 2023. Wato dai APC za ta tsayar da ɗan takara kenan daga kudu.
Badaru wanda shi ma ya na cikin ‘yan takarar shugaban ƙasa, ya ce har yanzu Buhari bai bayyana matsayar sa a kan amincewa ko rashin amincewa da hakan ba.
Badaru ya ce maganar gwamnoni Arewa sun amince, bai tayi ne su ka miƙa, ba a kai ga daddalewa ba tukunna.
Badaru ya ce ya yi mamakin da ya ji “wai an raba takardar bayan taro mai ɗauke da sa hannun mutane, wadda a maganar gaskiya ba haka abin ya ke ba.
“Mu tayi ne mu ka miƙa wa Baba Buhari, idan ya ga hakan ne mafita kuma ya amince, shikenan, sai a yi hakan. Idan kuma bai amince ba, sai mu ci gaba a kan tsarin da mu ke. Amma dai mu gwamnonin Arewa mu ka goyon bayan duk wata matsaya da Buhari ya bijiro da ita.”
Ya ce Gwamnonin Arewa sun wakilta Gwamna Atiku Bagudu na Kebbi da Simon Lalong na Filato da Abdullahi Sule na Nasarawa su je su sanar wa Shugaba Buhari cewa sun yarda duk ɗan Arewa mai takara a APC, to ya janye a bar wa ‘yan kudu su fito da ɗan takara a cikin su.
“Gaskiya ne Gwamnonin Arewa kamar su 11, ciki har da Ni mun tattauna wannan batu, sannan mu ka aika wa Shugaba Buhari cewa mun yi la’akari da halin da ake ciki, saboda haka mun yarda a bai wa ‘yan kudi takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin APC.”
“Maganar janyewa ta kuwa, ba za ni yi gaggawar janyewa ba, har sai na ji matsayar da Shugaba Buhari ya fitar.”
Wato dai kenan har yanzu dukkan ‘yan takarar 23 kowa na ciki, ko ɗaya bai janye ba.
APC Ta Nuske: Shugabannin jam’iyya sun yi fatali da Sanata Lawan, sun goyi bayan gwamnoni cewa a bai wa kudu takara:
Shugabannin Jam’iyyar APC sun ce ba su goyon bayan a bai wa Sanata Ahmad Lawan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin APC kai-tsaye ba.
Sakataren Tsare-tsaren APC na Ƙasa, Suleiman Argungu ne ya bayyana haka.
Argungu da wasu mambobin kwamitin shugabannin APC su huɗu ne su ka yi wa manema labarai jawabi a ranar Litinin, biyo bayan rahotannin da ke nuna cewa wai an ɗauki Lawan a matsayin ɗan takarar da jarjejeniya ta amince da shi.
Amma kuma tabbatattun rahotanni sun nuna Shugaban APC Abdullahi Adamu ya ambaci amincewa da Sanata Lawan ɗin.
Sai dai Argungu ya ce batun wai an ɗauki Lawan ɗan takara, ba tabbataccen batu ba ne, domin ba a tattauna lamarin a wurin taro ba.
Ya ce kawai bayani ne daga bakin shugaban jam’iyya, amma ba daga uwar jam’iyya ba.
Ya ci gaba da cewa ai Abdullahi Adamu ya na da ‘yancin faɗar ra’ayin sa kamar kowa.
“Magana ce kawai ta fatar bakin Abdullahi Adamu, amma ba mu tattauna ta a wurin taro ba.”
Mu a matsayin mu na Shugabanni ko Kwamitin Gudanarwa, mu na goyon bayan matsayar da gwamnonin APC na Arewa su ka cimma, wato mun amince a miƙa takarar shugaban ƙasa a APC ga Kudu kawai.” Inji shi.
Rikicin Bola Tinubu Da Fadar Shugaban Ƙasa:
Ba Kai Ne Ka Silar Buhari Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba -Fadar Shugaban Ƙasa:
Fadar Shugaban Ƙasa ta maida wa Bola Tinubu raddi, kwanaki huɗu bayan ya yi wa Shugaba Muhammadu Buhari gorin cewa ya yi takara sau uku ya na faɗuwa, sai da Tinubu ya mara masa baya sannan ya yi nasara a 2015 da 2019.
Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labaran Shugaba Buhari, Garba Shehu ya fitar, ya ce miliyoyin ‘yan Najeriya ne su ka zaɓi Buhari, ba wai mutum ɗaya ba.
Shehu ya ce mutane da dama sun taimaka wajen yi rawar ganin Buhari ya zama shugaban ƙasa, kuma akwai manya da ƙanana sosai.
Ya ce wannan gagarimar nasara ta kafa tarihin da a karon farko ɗan adawa ya kayar da shugaban da ke kan mulki a ƙasar nan.
A ranar Asabar dai Tinubu ya fitar da sanarwar cewa ya na ganin girma da mutuncin Shugaba Muhammadu Buhari.
Ya ce ba a yi wa jawabin da ya yi da Yarabanci kyakkyawar fassara ba.
Garba Shehu ya bayyana jawabin da Tinubu ya yi cewa ba abin mamaki ba ne.
“Tun da farko akwai waɗanda su ka shawarci shugaban ƙasa cewa ya sake tsayawa takara, duk kuwa da ya faɗi sau uku.
“Waɗannan su ne waɗanda su ka ga akwai buƙatar a kafa wata jam’iyya, wato APC, wadda za ta iya kasancewa motar da za a hau a kai ga nasara a inda gamayyar jam’iyyun adawa ha su kai ga nasara ba kafin ita.”
Shehu ya ce wannan tunani ya samu karɓuwa a zukatan miliyoyin jama’a, har su ka zaɓi APC ta yi nasara.”
Raddin Shehu ya zo ne daidai a ranar jajibirin Gangamin APC, wanda za a zaɓi ɗan takarar shugaban ƙasa.
Tinubu na cikin ‘yan takara 23 da ke nema. Kuma Abuja ta cika ta batse da mahalarta gangamin, inda tun daga ranar Lahadi ake ta ƙulle-ƙullen neman yadda za a fitar da ɗan takara ba sai a kai ga yin zaɓe ba.
Gwamnonin Arewa na APC dai sun amince a bai wa Kudu takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar kawai a wuce wurin.
Sai dai kuma kalaman Shugaban APC Abdullahi Adamu da ya ce sun yarda a bar wa Sanata Lawan daga Arewa takara, ya tayar da ƙura, har shugabannin APC sun ce ba su amince da maganar ta sa ba, domin ba a tattauna haka a wurin taro ba.
Discussion about this post