• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

MATAIMAKIN SHUGABAN ƘASA: Dalilin da ya sa Atiku ya ƙi ɗaukar Gwamna Wike

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 20, 2022
in Babban Labari
0
MATAIMAKIN SHUGABAN ƘASA: Dalilin da ya sa Atiku ya ƙi ɗaukar Gwamna Wike

Bayanai na ci gaba da fitowa fili dangane da dalilin da ya sa ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin PDP, Atiku Abubakar bai ɗauki Gwamna Nyesom Wike matsayin mataimakin takarar sa ba, sai ya ɗauki Gwamna Ifeanyi Okowa na Delta.

Wike dai shi ne ya zo na biyu a zaɓen, wanda Atiku ya zo na ɗaya. Ya na daga cikin gwamnoni uku da jiga-jigan PDP su ka bai wa Atiku sunayen su domin ya ɗauki ɗaya daga cikin su. Sauran su ne Ifeanyi Okowa Gwamnan Delta da kuma Udom Emmanuel na Akwa Ibom.

Dukkan waɗannan ukun daga 2023 sun kammala zango na biyu na mulkin su a matsayin gwamnoni.

Atiku ya shaida wa manyan PDP cewa ba zai iya ɗaukar Wike ba, saboda baya ga cewa shi ne abokin kafsawar sa a zaɓen fidda gwani na 2023 ɗin.

Sannan kuma ya shaida masu cewa Wike ya yi ƙoƙari ya kayar da Atiku a takarar zaɓen fidda gwani a 2018, inda shi Wike ya goyi bayan Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto a wancan lokacin.

Sai dai kuma siyasa ta raba Tambuwal da Wike a zaɓen fidda gwani na 2022, inda Tambuwal ya janye wa Atiku kuma ya umarci mabiyan sa su zaɓi Atiku.

Wannan tuggu da Tambuwal ya shirya shi ne ya kayar da Wike, wanda bayan kammala zaɓe ya kira Tambuwal da ire-iren su maciya amana.

Majiya ta ce duk da Atiku ya kai ziyarar neman goyon baya a gidan Wike, a Abuja bayan kammala zaɓe, har Wike ya yi alƙawarin taimaka wa Atiku a zaɓen shugaban ƙasa, majiya ta ce hankalin Atiku ya tashi, ganin yadda bayan Wike ya koma Fatakwal ya riƙa antaya maganganu masu zafi kan gwamnonin da su ka zaɓi Atiku, musamman Tambuwal da Ifeanyi Okowa.

Wike ya ji haushin yadda Tambuwal ya kware masa baya, domin shi Wike a 2018 ya goya wa Tambuwal ɗin baya.

Sannan kuma Wike ya ji takaicin abin da Okowa ya yi, wato goyon bayan Atiku.

Dalilin haushin kuwa shi ne, Gwamna Okowa ne jagaba wajen gwagwarmayar da gwamnonin kudu su ka riƙa yi a baya cewa tilas sai ɗan kudu za a bai wa takara.

Tunda kuwa Wike ya fito takara, ya na ganin bai ga dalilin da zai sa Okowa ya umarci dukkan daliget na Delta su zaɓi Atiku.

Sannan kuma Atiku na zargin cewa Wike ya yi rigima da tsohon shugaban PDP na ƙasa, Uche Secondus ne, saboda Secondus ɗin ya kusanci Atiku sosai da sosai.

Wasu manyan PDP na ganin idan aka bai wa Wike takarar mataimakin shugaban ƙasa, hakan zai kakketa PDP, maimakon ƙara ɗinke ɓarakar jam’iyyar.

PREMIUM TIMES Hausa ta yi nazaein Abin da ɗaukar Ifeanyi Okowa zai janyo wa takarar Atiku a zaɓen 2023.

A ranar Alhamis da rana ce ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya gabatar da Gwamnan Delta Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakin takarar shugaban ƙasa ɗin sa a zaɓen 2023 mai zuwa.

Ɗaukar Ifeanyi Okowa matsayin mataimakin takarar shugaban ƙasa na PDP zai haifar da abubuwa da dama, waɗanda ko dai su kai Atiku ga nasara, ko kuma ya ƙara shan kaye, kamar yadda ya sha a baya har sau uku a zaɓen shugaban ƙasa.

Ko ma dai me kenan, lamarin zai yi tasiri ne ko rashin yin tasiri, bisa la’akari da irin yadda yi amfani da abubuwan.

Da farko dai masu ruwa da tsaki na yi wa Okowa kallon cewa natsatstsen mutum ne kuma kamili, ba kamar Gwamna Nyesom Wike da ake wa kallon ɗan gidoga ko ɗan hauragiya da harigido ba.

Can a jihar Delta dai lamarin siyasar za ta iya canjawa idan PDP ta samu nasarar kama mulki. Domin tun daga 1999 har yau tsohon Gwamna James Ibori ne ke yin uwa-makarɓiya wajen naɗa wanda zai yi gwamna a jihar.

Shi kan sa Okowa yaron gidan siyasar James Ibori ne, saboda a 1999 zuwa 2007 ya yi kwamishina ƙarƙashin gwamnatin James Ibori. Kuma ya yi Sakataren Gwamnatin Jihar Delta a zamanin gwamnatin Emmanual Uduiaghan.

Cikin 2011 Okowa ya ci zaɓen Sanata na Delta ta Arewa.

Sai dai kuma an samu saɓani a wannan zaɓen fidda-gwani na wanda zai gaji Okowa a gwamnan Delta ƙarƙashin PDP. Wanda Ibori ke so daban, shi ma Gwamna Okowa wanda ya ke so daban. Dukkan su kuma ƙabilar Urhobo ne, tushen James Ibori.

A ƙarshe dai ɗan takarar da Okowa ke so ya kayar da ɗan takarar da Ibori ke su. An ce Ibori ya fusata, har ya yi alƙawarin idan zaɓe ya zo sai ya shuka wa PDP ko kuma ɗan takarar tana jihar tsiya.

To yanzu dai tunda an zaɓi Okowa ɗan takarar mataimaki, jam’iyyar PDP ta koma a hannun sa kenan a jihar Delta, maimakon ubangidan sa James Ibori.

Abu na biyu shi ne ana ganin matsayin Okowa ɗan asalin ƙabilar Igbo, hakan zai iya yayyafa wa yankin Kudu maso Gabas ruwan sanyi, su haƙura su goyi bayan PDP, tunda dai ba su samu damar tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa ba a manyan jam’iyyu biyu, APC da PDP.

Amma shi kuwa Wike, ba sau ɗaya ko sau biyu ba ya sha nesanta kan sa ko asalin sa daga kabilar Igbo.

Sannan an ce Wike ne ya riƙa sukar Peter Obi har ya harzuƙa shi, ya fice daga PDP, ya koma LP ya fito takarar shugaban ƙasa.

Okowa bai cika surutai ko bobbotai irin na Wike ba. Ana ganin Wike ya yi katoɓara a shekarun baya da ya ce “Jihar Ribas ta Kiristoci ce zalla.”

Shi kuwa Gwamna Okowa babu ruwan sa da shiga-sharo-ba-shanu, ko yin uwa-makarɓiyar rigingimun siyasa, kamar yadda Gwamna Wike ke yi, har abin ya zame masa jiki.

Babban aikin da ke gaban Okowa shi ne yadda zai samar wa PDP ƙuri’u a Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma da Kudu maso Kudu. Zai iya yin bakin ƙoƙarin sa, musamman tunda bai taɓa shiga hancin manya da ƙudundune ba.

An haifi Okowa a cikin 1959 a garin Owa-Alero, cikin Ƙaramar Hukumar Ika ta Arewa maso Gabas.

Sai dai kuma masu nazarin siyasa da dama na ganin a yanzu PDP za ta iya rasa ɗimbin ƙuri’un magoya bayan Gwamna Wike, ganin yadda ya samu ƙuri’u da dama a zaɓen fidda gwani.

Su na ganin da shi aka ɗauka, zai fi karɓuwa har a Arewa sosai. Domin a cewar da dama, ba a san Ifeanyi Okowa a Arewa ba.

Ya yi kwamishina zamanin mulkin James Ibori, ya yi Sakataren Gwamnatin Jiha zamanin mulkin Emmanual Uduiaghan, kuma ya yi sanata kafin ya zama gwamna.

Tags: AbujaAtikuHausaNewsPDPPREMIUM TIMESWike
Previous Post

Sai APC ta naɗa Zulum ko El-Rufai mataimakin Tinubu, idan ana so ta samu ƙuri’u a Arewa – Masu Ruwa da Tsakin APC

Next Post

‘Yan bindiga sun kai hari wasu coci biyu, sun kashe mutum uku, sun yi garkuwa da mutane da dama daga Kaduna

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
ZAMFARA: ‘Yan bindiga sun kashe mutum biyar a kauyen Rogoji a lokacin sallar Asuba

'Yan bindiga sun kai hari wasu coci biyu, sun kashe mutum uku, sun yi garkuwa da mutane da dama daga Kaduna

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi
  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.