• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    MATA KU RIKA SAKA JIGIDA: Sirrika 6 da saka jigida ke yi wa mace – Binciken Masana

    MATA KU RIKA SAKA JIGIDA: Sirrika 6 da saka jigida ke yi wa mace – Binciken Masana

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    Yadda rundunar sojin sama suka kashe fitaccen dan bindiga, matan sa biyu da kwamandojinsa 8 a Katsina

    A shafe tarihin wadanda suka soke koyar da tarihi a makarantun Najeriya – Wole Soyinka

    Wole Soyinka ya yi tir da bidiyon barkwanci da shegantakar ‘yan ƙungiyar ‘Pyrates Confraternity’ kan Tinubu

    Duk masu son shugabancin Najeriya su fito su nuna fuskokin su, ba sai lokaci yayi a hadamu da tarkace ba – Muhammadu Sanusi II

    Cire ni daga Sarautar Kano ba zai hana ni ci gaba da faɗin gaskiya ba – Sanusi Lamiɗo

    NDLEA

    Jami’an NDLEA sun kama Faston Coci da durum uku cike makil da muggan kwayoyi

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Ƴan sanda sun kama mutumin da ya saba Yi wa mata fashi bayan ya zuba musu maganin barci a lemu

    Na zaɓi wanda zai yi mini mataimaki, sunan sa na nan a ƴar takarda a gaban aljihuna na cakale – Tinubu

    Lauya ya maka INEC kotu, saboda zargin akwai dungu cikin fam ɗin takarar da Tinubu ya cike

    Ana batakashi tsakanin ‘yan ta’adda da Sojojin Najeriya a Madallah Abuja

    Najeriya ta tsaurara tsaron kurkukun Katsina, Kebbi da Gusau, don hana farmakin ‘yan ta’adda

    Dalilin tsadar abinci a Najeriya da matakan da mu ke shirin ɗauka -Ministan Gona

    Dalilin tsadar abinci a Najeriya da matakan da mu ke shirin ɗauka -Ministan Gona

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    MATA KU RIKA SAKA JIGIDA: Sirrika 6 da saka jigida ke yi wa mace – Binciken Masana

    MATA KU RIKA SAKA JIGIDA: Sirrika 6 da saka jigida ke yi wa mace – Binciken Masana

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    Yadda rundunar sojin sama suka kashe fitaccen dan bindiga, matan sa biyu da kwamandojinsa 8 a Katsina

    A shafe tarihin wadanda suka soke koyar da tarihi a makarantun Najeriya – Wole Soyinka

    Wole Soyinka ya yi tir da bidiyon barkwanci da shegantakar ‘yan ƙungiyar ‘Pyrates Confraternity’ kan Tinubu

    Duk masu son shugabancin Najeriya su fito su nuna fuskokin su, ba sai lokaci yayi a hadamu da tarkace ba – Muhammadu Sanusi II

    Cire ni daga Sarautar Kano ba zai hana ni ci gaba da faɗin gaskiya ba – Sanusi Lamiɗo

    NDLEA

    Jami’an NDLEA sun kama Faston Coci da durum uku cike makil da muggan kwayoyi

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Ƴan sanda sun kama mutumin da ya saba Yi wa mata fashi bayan ya zuba musu maganin barci a lemu

    Na zaɓi wanda zai yi mini mataimaki, sunan sa na nan a ƴar takarda a gaban aljihuna na cakale – Tinubu

    Lauya ya maka INEC kotu, saboda zargin akwai dungu cikin fam ɗin takarar da Tinubu ya cike

    Ana batakashi tsakanin ‘yan ta’adda da Sojojin Najeriya a Madallah Abuja

    Najeriya ta tsaurara tsaron kurkukun Katsina, Kebbi da Gusau, don hana farmakin ‘yan ta’adda

    Dalilin tsadar abinci a Najeriya da matakan da mu ke shirin ɗauka -Ministan Gona

    Dalilin tsadar abinci a Najeriya da matakan da mu ke shirin ɗauka -Ministan Gona

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Kotun Ƙoli ta yi fatali da ƙarar da Buhari da Malami su ka shigar kan ƙalubalantar Sashen 84(12) na Dokar Zaɓe

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 24, 2022
in Babban Labari
0
An bankado wasu gaggan ‘yan Najeriya dake daukar nauyin’ Yan ta’adda da ta’ addanci a kasar nan – Malami

Babbar Kotun Tarayya ta hamɓarar da ƙarar da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da Ministan Shari’a Abubakar Malami su ka shigar, wadda wadda su ka ƙalubalanci Sashe na 84(14) na Sabuwar Dokar Zaɓe.

Manyan Alƙalai bakwai ne su ka zartas da hukuncin, bisa shugabancin Mai Shari’a Musa Dattijo-Muhammad, gaba ɗayan su sun amince da korar ƙarar, sun kuma kira ƙarar cewa Buhari da Malami na ƙoƙarin yi wa kotu karan-tsaye.

Mai Shari’a Aokmaye Agim ne karanta sakamakon hukuncin, inda ya bayyana cewa “tunda dai har Buhari ya saka wa Sabuwar Dokar Zaɓe ta 84(12) ta 2022 hannu, to ba shi da wani dalili ko hujjar da zai garzaya kotu ya nemi a soke dokar, bayan ya saka mata hannu.

“Babu wani wuri a cikin Kundin Dokokin Najeriya inda doka ta ba Shugaban Ƙasa ikon ya nemi kotu ta sake wata doka, bayan ya rigaya ya sa mata hannu. Haka kuma babu dokar da ta ba Shugaban Ƙasa ikon ya nemi kotu ta maido wata dokar da shi shugaban ya ƙi sa mata hannu, bayan wa’adin sa mata hannun ya wuce.” Inji Mai Shari’a Agim.

Kotu Ƙoli ta ci gaba da cewa hatta roƙon da Shugaba Buhari ya yi wa Majalisa a Najeriya, inda ya nemi su goge dokar bayan ya rigaya ya sa mata, shi ma haramtacce ne, kuma ya karya doka.

Agim ya ce Buhari da Malami sun shigar da ƙara don kawai a tunanin su kotu za ta amince da soke wata dokar da Buhari ya yi.

Wannan kuwa inji shi ba abin saurare ha ne a kotu, bisa la’akari da Sashe na 1(1) (a) na Ƙarin Ƙarfin Ikon Kotun Ƙoli.”

Sauran mambobin Alƙalan da su ka fatattaki Buhari da Malami daga kotu, sun haɗa da Dattijo Muhammad, John Okoro, Amina Augie, Lawal Garba da Ibrahim Saulawa.

Dajin Da Aka Keto Kafin Kotun Ƙoli Ta Kori Ƙarar Da Buhari Da Malami Su Ka Shigar:

Idan ba a manta ba, Buhari da Minista Malami sun maka Majalisar Tarayya Kotun Ƙoli saboda fatawar Sashen 84(12) na Sabuwar Dokar Zaɓe.

Shugaba Muhammadu Buhari da Ministan Shari’a Abubakar Malami, sun garzaya Kotun Ƙoli, su na neman a yi masu fassara da sharhin ma’anar wani sashe na Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022.

Buhari da Malami sun shigar da ƙarar tun a ranar 29 Ga Afrilu, inda su ka maka Majalisar Dattawa da Majalisar Tarayya kotu.

Sashe na 84(12) na Sabuwar Dokar Zaɓe dai ya shiga harankazamar ja-in-ja a Najeriya, tun bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya sa wa Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022 hannu cikin watan Fabrairu.

Jim kaɗan bayan Buhari ya sa wa ƙudirin dokar hannu ta zama doka, ya roƙi Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa cewa su soke wancan sashe da ake ta tankiya a kan sa, amma su ka yi ƙememe, su ka ƙi goge shi.

Abin Da Sashe Na 84(12) Ya Ƙunsa:

“An haramta wa mai riƙe da muƙamin siyasa ko muƙamin gwamnati ko shugabancin jam’iyya yin zaɓe a matsayin wakilin masu zaɓen ‘yan takara. Kuma ba a yarda a zaɓe shi ba, sai da idan ya ajiye muƙamin sa.”

Idan ba a manta ba, watanni biyu da su ka gabata, Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia a Jihar Abiya ta soke wannan sashe na 84(12), bisa dalilin cewa ya ci karo da Kundin Dokokin Najeriya.

Shawagin-ɓiɗar-kaɗen Minista Malami:

Minista Malami ya yi azarɓaɓin cewa zai soke dokar domin bin umarnin Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia. Sai dai kuma a lokacin ya na da kwaɗayin takarar gwamna a jihar Kebbi.

Kafin Malami ya soke dokar, sai Kotun Ƙoli ta yi gaggawar soke hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia ta zartas. Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce kada a sake a soke dokar.

Ganin haka ne a yanzu Buhari da Malami su ka dira Kotun Ƙoli, domin a san matsayar wannan Sashe na 84(12) da ke cikin Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2023.

A makon jiya ne Premium Times ta buga labarin yadda Majalisar Tarayya Ta Bi Ra’ayin Majalisar Dattawa, Su Ka Yi Wa Sashe Na 84 (8) Na Sabuwar Dokar Zaɓe Kwaskwarima:

Majalisar Tarayya ta amince tare da aikawa da kwaskwarimar da su ka yi wa Sabuwar Dokar Zaɓe Sashe na 84 (8) na 2022, ta yadda wakilan zaɓen ‘yan takara masu riƙe da muƙaman gwamnati za su samu damar yin zaɓen fidda-gwani, taron gangami da tarukan jam’iyya.

Majalisar Tarayya ta yi wa sabuwar dokar kwaskwarima ce bayan ta yi la’akari da Kudirin da Shugaban Kwamitin Majalisa Abubakar Fulata ya gabatar a ranar Laraba, a Abuja.

Kudirin dai mai suna, “Kudirin Yin Kwaskwarima Ga Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022 Mai Lamba 13”, ya bayar da dama ga wakilan jam’iyya masu riƙe da muƙaman gwamnati su yi zaɓe a lokacin zaɓukan fidda-gwanin ‘yan takarar jam’iyyu.

Idan an tuna, Sabuwar Dokar Zaɓe wadda Shugaba Muhammadu Buhari ya sa wa hannu cikin watan Fabrairu 2022, ta haramta wa masu riƙe da muƙaman gwamnati su yi zaɓen fidda gwani.

Su Wane Ne Masu Riƙe Da Muƙaman Siyasa?:

Sun haɗa da: Kansilolin mazaɓu da ke ƙananan hukumomi, shugabannin ƙananan hukumomi da mataimakan su, shugabannin jam’iyyu na ƙananan hukumomi 774, ‘yan majalisar dokokin jihohi da ‘yan majalisar tarayya.

Sauran sun haɗa da: Gwamnoni, mataimakan gwamnoni, shugaban ƙasa da mataimakin sa, Shugabannin Majalisar Gudanarwar Jam’iyya, shugabannin jam’iyya na jihohi, na ƙananan hukumomi da sakatarorin su.

Wannan sabuwar doka da aka yi wa kwaskwarima za ta bai wa waɗannan da aka lissafa a sama su yi zaɓen ‘yan takara a zaɓen fidda gwani.

Idan ba a manta ba, Majalisar Dattawa ta amince da wannan kwaskwarima tun a ranar 10 ga Mayu, 2022.

A farkon shekarar nan PREMIUM TIMES Hausa ta riƙa kawo kwatagwangwamar da ta dabaibaye wannan sabuwar doka. Har ta kai an bada wani rahoton da babban lauya Femi Falana ya zargi Ministan Shari’a Abubakar Malami da yin surunkutumi cikin sha’anin hukuncin kotu.

‘Yadda Ministan Shari’a Malami ya damalmala hukuncin kotu a kan Dokar Zaɓe’ -Femi Falana:

Babban Lauya mai rajin kare haƙƙi da ‘yancin jama’a Femi Falana ya zargi Ministan Shari’a Abubakar Malami da damalmala Babbar Kotun Tarayya ta yadda ta bayar da hukunci baddalalle mai cike da tarnaƙi akan matsayar sashe na 84(12) na Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022.

Falana ya ce Malami ya yi bakam, ya nuna kamar bai ma san akwai wani hukunci ko umarnin kotu wanda na Kotun Tarayya wanda ya haramta masa yin katsalandan a kan dokar. Amma sai ya jajirce cewa shi sai ya yi amfani da umarnin Babbar Kotun Umuahia, wadda ta bayar da umarnin a soke wannan sashen ɗungurugum.

Falana wanda babban lauya ne (SAN), ya fitar da sanarwa inda ya bayar da cikakken bayanin yadda Manyan Kotunan Tarayya guda uku suka bayar da mabanbantan hukunce-hukunce. Daga nan Falana ya ɗora laifin gaba ɗaya a kan Ministan Shari’a Malami.

“Don haka sai Falana ya ce ya kamata Malami ya sani cewa ba fa zai iya yin yadda ya ga dama ba, ta hanyar bin umarnin da ya ga dama, kuma ya bijire wa wadda ya gada dama.

“Sannan kuma babu sauran wata jikara ko tantama, tabbas Ministan Shari’a ya damalmala hukuncin Babbar Kotun Tarayya har ta bayar da baddalallun hukunce-hukunce a kan sashe na 84(12) na Dokar Zaɓe ta 2022.” Inji Falana.

Tags: AbujaBuhariDokaHausaINECKorumalamiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESƘoli
Previous Post

MATAIMAKIN SHUGABAN KASA 2023: Kwankwaso zai gana da Wike a Fatakwal

Next Post

ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

Next Post
Petrol Tankers

ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda Sheikh Gumi yayi ruwa ya yi tsaki aka saki ɗan tsohon gwamnan Kano da iyalan sa daga ƴan ta’adda
  • Wawanci da shashanci ke sa wasu na kwaikwayon tangaɗi, rangaji da karkarwar hannun Tinubu -Sanatan PDP
  • Majalisar Tarayya ta umarci Ministar Kuɗaɗe ta bada takardar bayanan biyan kuɗaɗen tallafin fetur daga 2013 zuwa 2022
  • Ina nan da rai na cikin koshin lafiya gadagau – Kabiru Nakwango
  • ‘Yan sanda sun kama ƴan IPOB da ake zargi da kisan ‘yan sanda hudu a jihar Imo

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.