Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai
Assalamu Alaikum
‘Yan uwa masu girma, kamar yadda muka yi rubutu jiya, muka yada da harshen turanci, domin jawo hankalin al’ummah, gashi ma a yau zamu yada da yaren Hausa. Kamar yadda kuka sani, akwai wani rubutu da wani mai suna Sanusi Mohammed ko Mohammed Sanusi wanda yake yin rubutu a kafafen yada labarai na zamani wato social media, yana sukar ‘yan siyasa, yana zage-zage da cin mutuncin wasu ‘yan siyasa, amma wasu mutane, wadanda suke da wata manufa a rayuwar su, da wadanda basu san waye mai yin rubutun ba, sai su rinka yada wannan rubutu, suna cewa wai Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II shine yake yin wannan rubutu.
Mun sha sanar da duniya, ba sau daya ba, ba sau biyu ba cewa, tabbas Sarki Sanusi baya son zalunci, baya son rashin gaskiya, kuma baya so a cuci al’ummah, ko a cuci talaka, to amma shi gaskiya kawai yake fada har idan zai fada. Baya zagin kowa, baya cin mutuncin kowa, baya yiwa kowa karya, baya yiwa kowa sharri da kazafi da kage. Domin shi wannan ba hanyar sa bace ko kadan.
Saboda haka muke ta kokarin jawo hankalin al’ummah cewa su sani, kokarin da wasu suke yi na dangata rubuce-rubucen wancan mutum mai suna Mohammed Sanusi zuwa ga Sarki zalunci ne babba. Don haka sai mu kiyaye don Allah!
Don haka muna kara jawo hankalin al’ummah baki daya cewa, mai yin wannan rubutu, mai suna Mohammed Sanusi, ba Khalifah Sarki Muhammadu Sanusi II bane. Kawai wani mutum ne, dan social media yake yin wannan rubutu.
Kuma abun bakin ciki, shi rubutun wannan mutum, wato Mohammed Sanusi, za ka ga har da wasu manyan ‘yan siyasa suke yada shi, domin cimma wata manufa ta su! Kamar yadda muka ga Mista Doyin Okupe yana yada wannan rubutu na karya, har yana cewa wai daga Khalifah wannan rubutu yake, wanda wallahi, wannan karya ne, ba gaskiya bane sam. Don haka don Allah mutane mu kara kiyaye wa.
Ga rubutun nan na hada dashi anan, domin mutane su kara gani, ba tare da na canza komai ba, ko na kara wani abu, ko na rage:
“See Sanusi describing our Presidential candidates
One peculiar thing about the top three guys battling it out for the 001 seat, is that neither of them is there for the money.
One has milked Nigeria well enough systematically, and just wants to answer President by all means. He lives in Dubai full-time and only comes around every 4 years to contest for the Presidency.
He doesn’t understand the struggle of the average Nigerian. He doesn’t care so much. If he loses this one, he will go back to Dubai and wait out the next 4 years before coming out again.
Besides the fact that his ambition is scary, we can’t afford to have a Paul Biya of Cameroun as President.
Another has been controlling Lagos treasury since 2003. He just wants to fulfill his lifetime political ambition of answering President, even if he dies the next day after swearing-in.
He would properly share Nigeria like cake to his boys….just like he did in Lagos. At the end of the day, he would teach us what being “fantastically corrupt” actually means.
The other was already a billionaire before 2003, and quite content with himself. He doesn’t need your money for anything. He wants to be President to reset things and lay the foundation for systemic governance in future.
He relates with the struggles of the average Nigerian, understands what Nigeria needs, and has volunteered himself to save us from impending catastrophe. Win or lose, he would most likely not contest again.
It is up to us to choose wisely.
~ Mohammed Sanusi
Wannan shine rubutun asalin, Allah yasa mu dace, amin.
Wassalamu Alaikum,
Dan uwan ku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, daga Okene, jihar Kogi, Najeriya. Lahadi, 19/06/2022. 08038289761.
Discussion about this post