Ranar Dimokaradiyya ba kawai rana bace ta yin murnar zagayowar ta, rana ce da ýan kasa za su yi nazari da karatun nutsuwa na nasarori da kalubalen da a ka fuskanta na tsawon lokacin, da kuma maida hankali da yanayin da a ke ciki a yau, sannan a fito da kiran da za a yi wa ýan kasa don samun mafita a ciki.
A baya kafin Nijeriya ta dawo mulkin dimokaradiyya a 1999, an ta’allaka rashin cigaban Nijeriya, barazanar tsaro, cin hanci da rashawa a kan dadewar da kasar ta yi a karkashin mulkin soja.
Amma a yau zamu iya kirga riba a fannin tsaro da nasara a kan Cin-Hanci da Rashawa tun lokacin da a ka dawo dimokaradiyya kawo yau?
Wai APC da kawarta PDP na da bakin magana a kan kalubalen Rashawa da Tsaro a Nijeriya?
Duk da murnar da ýan Nijeriya suka yi na dawowar mulkin dimokaradiyya da kuma nishin farko da Shugaba Obasanjo yayi a lokacin mulkinsa na shawo kan rikicin Bakasi, rikicin Niger Delta, Zaki Biyam a fuskar tsaro, da kuma fusatar sa ta yakar cin hanci da rashawa wajen kafa hukumomi irin su EFCC, ICPC da makamantan su, wadannan yunkuri ya sakawa yan Nijeriya nutsuwar cewa za su ci gajiyar mulkin Dimokaradiyya.
Amma, kash! Sai gashi manyan yan siyasar PDPn da jamián gwamnati ana ta tuhumar su da cin hanci da rashawa, babban ma abin tashin hankali shine sai gashi a na tuhumar su da karkatar da kudden da aka ware domin sayen makaman da za a yaki rashin tsaron da ke addabar kasar, wanda wannan a mahanga ta tunani yafi komai muni da cin amanar dimokaradiyya da kasa.
Ita kanta Jam’íyyar APCn karatun ta akan cin hanci da rashawa abin kunya ne da takaici, babban abin mamakin ma shine, yan Nijeriya sun goyi bayan APC don gazawar da PDPn tayi wajen samar da tsaro da yaki da cin hanci da rashawa, sai ga shi ana zaton wuta a makera sai ta tashi a masaka.
Abin takaici ma shine a wannan karni sai gashi a na tuhumar shugaban hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa EFCC na baya shima da zargin rashawar, wanda dole a ka dakatar da shi, sai dai abu mai kamar wasan kwaikwayo sai gashi a bibiyar labarai a kan al’amarin, sai ya zamanto kamar da shi da ministan sa kawai rigima ce a kan cin mushe.
Wata sabuwa a kwanakin nan sai gashi a na tuhumar Babban Akawun Nijeriya AGoF da sama da fadin har na sama da Naira Miliyan Dubu Tamanin, duk da kasancewar ya samu yabo a baya har a ka kara masa lokacin aiki duk da ya kamata yayi ritaya.
Nazari a kan Tsaro kuwa, bayan ‘yan Nijeriya sun gujewa PDP don neman tsaro sai ga shi a yau a na lissafin Nijeriya bata taba shiga na yanayin rashin tsaro ba kamar na wannan lokacin, wasu ma na cewa a kullum sai an kasha mutane sama da ashirin, dalilin ta’addanci.
To kuma me nene, shin wannan lokaci ne na murnar zagayowar 12 ga watan Yuni ko kuma na karatun ta nutsu da neman hanyar fidda kasar nan daga mummunan mulkin dimokaradiyya da muke fama da ita.
Ýan PDP da APC su suka jagorancin kasar a tsawan wannan lokaci, jagororin su suka fi kowa jin dadi da samun rayuwa ta nutsuwa, amma talaka kuwa annobar mummunan mulki ya moda, talauchi da tsoro da koma baya ta rayuwa ita ya ke fuskanta.
PDP da APC ko mai zasu gaya mana a kan tsaro da rashawa?
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post